• English
  • Business News
Monday, June 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hafsan Soji Ya Gana Da Shugabanni A Filato Kan Hare-haren Da Suka Yi Ajalin Mutane

by Sadiq
2 months ago
in Labarai
0
Hafsan Soji Ya Gana Da Shugabanni A Filato Kan Hare-haren Da Suka Yi Ajalin Mutane
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Rundunar Sojin Nijeriya, Laftanar Janar Olufemi Oluyede, ya gana da shugabannin al’umma a Ƙaramar Hukumar Bokkos ta Jihar Filato, bayan hare-haren da aka kai wasu ƙauyuka da suka yi sanadiyar mutuwar mutane fiye da 50, tare da rushe gidaje sama da 300, tare da raba sama da mutane 1,000 da muhallansu. 

Ƙauyukan da lamarin ya shafa sun haɗa da Hurti, Ruwi, Josho, Daffo, Manguna da wasu da ke maƙwabtaka da su.

  • Harin Filato: An kashe Mutane 40, An Kona Gidaje 383, Fiye Da Mutane 1,000 An Raba Su Da Muhallansu 
  • Sabon Tsarin Harajin Kwastam Na Amurka Ya Kwace ‘Yancin Sauran Kasashe

A wajen taron, Laftanar Janar Oluyede ya buƙaci al’ummar yankin da su rungumi zaman lafiya da haɗin kai.

Ya ce dole ne a yi aiki tare domin samun zaman lafiya, ba wai a bar komai a hannun sojoji kaÉ—ai ba.

Ya kuma tabbatar da cewa sojojin Nijeriya za su ci gaba da zama masu adalci da kare kowa ba tare da nuna bambancin ƙabilanci ko addini ba.

Labarai Masu Nasaba

AlÆ™alai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

Shugaban sojin ya ce za a kamo waɗanda suka aikata wannan mummunan ta’asa, kuma za a hukunta su.

Haka kuma ya yi alƙawarin tura ƙarin jami’an tsaro zuwa yankunan da abin ya shafa domin kare rayuka da dukiyoyi.

A nasa jawabin, Manjo Janar Folusho Oyinlola, kwamandan Operation Safe Haven, ya ce za su ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro domin tabbatar da zaman lafiya musamman a lokacin girbin gonaki.

Ya bayyana cewa ganawar da shugabannin yankin na zuwa a lokaci mai muhimmanci duba da yadda matsalar tsaro ke ƙaruwa.

Dagacin Manguna, Alhaji Alo Raymond, ya ce hare-haren da ake kai musu na da nasaba da yunƙurin karɓe musu filayen gado.

Ya roƙi gwamnati ta kare su da gidajensu, tare da tallafa wa waɗanda abin ya shafa da abinci da sauran kayan buƙatu domin farfaɗo da rayuwarsu.

Wasu daga cikin mazauna yankin da suka halarci taron sun bayyana fatan cewa wannan ziyara da kuma alƙawuran da shugabannin tsaro suka yi za su haifar da zaman lafiya.

Sun kuma buƙaci gwamnatin tarayya da ta jiha da su ɗauki mataki gaggawa domin kawo ƙarshen wannan rikici da kuma tallafa wa waɗanda suka rasa matsugunnai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FilatoHare-HareTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Lakurawa Sun Kashe ’Yan Sa-kai 13 A Wani Sabon Hari A Kebbi

Next Post

Ya Kamata Lambar Yabo Ta Zama Hanyar Ƙarfafa Mana Gwuiwa – Misis Nda-Isaiah

Related

Labarai

AlÆ™alai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

11 minutes ago
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya
Labarai

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

2 hours ago
Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru
Manyan Labarai

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

3 hours ago
Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta
Manyan Labarai

Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

4 hours ago
2027: Ƙungiyar Shekarau Ta Gindaya Sharaɗi Kafin Shiga Haɗakar Jam’iyyu
Labarai

2027: Ƙungiyar Shekarau Ta Gindaya Sharaɗi Kafin Shiga Haɗakar Jam’iyyu

7 hours ago
Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa
Labarai

Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

17 hours ago
Next Post
Ya Kamata Lambar Yabo Ta Zama Hanyar Ƙarfafa Mana Gwuiwa – Misis Nda-Isaiah

Ya Kamata Lambar Yabo Ta Zama Hanyar Ƙarfafa Mana Gwuiwa – Misis Nda-Isaiah

LABARAI MASU NASABA

AlÆ™alai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

June 2, 2025
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

June 2, 2025
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

June 2, 2025
Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

June 2, 2025
Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

June 2, 2025
Manchester United Ta Kammala ÆŠaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

Manchester United Ta Kammala ÆŠaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

June 2, 2025
2027: Ƙungiyar Shekarau Ta Gindaya Sharaɗi Kafin Shiga Haɗakar Jam’iyyu

2027: Ƙungiyar Shekarau Ta Gindaya Sharaɗi Kafin Shiga Haɗakar Jam’iyyu

June 2, 2025
Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

June 1, 2025
Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

June 1, 2025
Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.