A yau Alhamis ne aka bude dandalin taron shekara-shekara na shekarar 2025 na tattaunawa na Asiya, a garin Boao na lardin Hainan dake kudancin kasar Sin.
Mataimakin firaministan kasar Sin Ding Xuexiang, wanda kuma memba ne a ofishin siyasa na kwamitin tsakiyar jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ya halarci bikin bude dandalin.
- Wang Yi Ya Gana Da Takwaransa Na Faransa
- Wakilin Sin: Dole Ne A Mutunta Hakki Mai Tushe Na Palasdinawa
Tun a shekarar 2001 aka kaddamar da dandalin na Boao, a matsayin dandalin da ba na gwamnati ba, da aka kafa ba don neman riba ba, wanda ke mayar da hankali ga ingiza dinkewar tattalin arzikin shiyyar, tare da kusantar da kasashen Asiya da kudurorinsu na ci gaba. A bana dandalin na gudana tsakanin ranakun 25 zuwa 28 ga watan nan na Maris, karkashin jigon “Asiya a duniya mai sauyawa: Cimma makomar bai daya.”
Gabanin bude dandalin, a jiya Laraba mataimakin firaministan kasar Sin Ding Xuexiang, ya gana da wasu manyan jami’ai na kasashen waje da suka ziyarci kasar Sin don halartar dandalin na Boao, ciki har da firaministan kasar Lao Sonexay Siphandone, da mataimakin shugaban kasar Micronesia Aren B. Palik, da mataimaki na farko na firaministan Mongolia, kuma ministan raya tattalin arzikin kasar Luvsannyam Gantumu.
Sauran sun hada da mataimaki na farko na firaministan kasar Kazakhstan Roman Sklyar, da ministan tsare-tsare a fannin raya ababen more rayuwa da samar da ci gaba na Indonesia Agus Harimurti Yudhoyono, da ministan cikin gida da harkokin waje na kasar Portugal Paulo Rangel. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp