• English
  • Business News
Saturday, September 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin 2024: NAHCON Ta Kaddamar Da Kwamitin Tantance Kamfanonin Jiragen Aikin Hajji

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Hajjin 2024: NAHCON Ta Kaddamar Da Kwamitin Tantance Kamfanonin Jiragen Aikin Hajji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta kaddamar da kwamitin tantance kamfanonin jiragen saman fasinja da na dakon kaya don aikin hajjin 2024.

Kamfanonin jiragen fasinja tara da na dakon kaya hudu ne su ka mika bukatar hidima ga alhazan Nijeriya domin aikin hajjin 2024.

  • Matakan Amurka Na Kayyade Fitar Da Matattarar Bayanai Ta Microchip Za Su Kawo Illa Ga Kasuwar Samar Da Kayan Ta Duniya
  • ‘Yansanda Sun Kama Darakta Da Wasu Mutane 2 Bisa Zargin Gwanjon Kayan Gwamnatin Kano

Shugaban NAHCON Malam Jalal Ahmed Arabi, ne ya kaddamar kwamitoci biyu; masu wakilai 32 domin tantancewa da su.

Jalal Arabi ya ce duk abin da a ke so a yi nasara to tabbas sai an fara shiri da wuri, domin tsadar farashin canjin dala ya zama kalubalen da a ke fafutukar daukar matakai don tabbatar da rangwame da walwalar maniyyata.

Sakataren hukumar kuma mukaddashin shugaban kwamitocin biyu, Dakta Abdullahi Rabi’u Kontagora, ya ja hankalin wakilan kwamitocin da su yi aiki tsakani da Allah.

Labarai Masu Nasaba

Matatar Dangote Ta Dawo Sayar Da Man Fetur A Kuɗin Naira

Ana Hasashen Tashin Fetur Idan Matatar Dangote Ta Daina Karɓar Naira

Ya ce: “Don tabbatar da duk kamfanin da a ka bai wa aikin yana da kayan aiki da muradin kare rayukan maniyyata.”

Daraktan kamfanin Max Air, Dikko Dahiru Mangal, ya ce a shirye su ke su tunkari kwamitin tantancewar.

“Muna da ingantattun kayan aiki don gudanar da wannan aiki.”

Malam Ahmad Bashir Bulma na kamfanin dakon kaya na hukumar jiragen Nijeriya da ke Legas, ya ce wannan ba shi ne karo farko da suke kula da jigilar kayan alhazai ba.

“Muna da dukkan takardun da a ke bukata don haka mu ke maraba da wannan tantancewa.”

Wannan ya dai biyo bayan matsayar da hukumomin Saudiyya da hukumar alhazan Nijeriya suka cimma, na amincewa da kara yawan kamfanonin jiragen yawo da za su shiga hidimar jigilar alhazai zuwa guda 40.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hajjin 2024Jiragen SamaKwamitiz JigilaNAHCON
ShareTweetSendShare
Previous Post

NLC Ta Yi Barazanar Sake Shiga Yajin Aiki

Next Post

An Shiga Firgici Bayan Sabon Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara

Related

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Matatar Dangote Ta Dawo Sayar Da Man Fetur A Kuɗin Naira

25 minutes ago
Ana Hasashen Tashin Fetur Idan Matatar Dangote Ta Daina Karɓar Naira
Manyan Labarai

Ana Hasashen Tashin Fetur Idan Matatar Dangote Ta Daina Karɓar Naira

8 hours ago
Majalisar Shura ta Kano Za Ta Binciki Zargin Batanci Ga Annabi Kan Malam Triumph
Manyan Labarai

Majalisar Shura ta Kano Za Ta Binciki Zargin Batanci Ga Annabi Kan Malam Triumph

13 hours ago
’Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi A Kaduna, Sun Ƙwato Bindiga Da Wayoyi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi A Kaduna, Sun Ƙwato Bindiga Da Wayoyi

1 day ago
NECO 2025: Gwamnan Kano Ya Bayyana Bayanai Ba Daidai Ba
Manyan Labarai

NECO 2025: Gwamnan Kano Ya Bayyana Bayanai Ba Daidai Ba

1 day ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Yadda Gwamnoni Suke Kawo Cikas
Manyan Labarai

‘Yancin Kananan Hukumomi: Yadda Gwamnoni Suke Kawo Cikas

2 days ago
Next Post
An Shiga Firgici Bayan Sabon Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara

An Shiga Firgici Bayan Sabon Harin 'Yan Bindiga A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Dawo Sayar Da Man Fetur A Kuɗin Naira

September 27, 2025
Shugaban Cuba Ya Yi Bayani Kan Nazarin Fasahohin Sin A Fannoni Shida

Shugaban Cuba Ya Yi Bayani Kan Nazarin Fasahohin Sin A Fannoni Shida

September 27, 2025
Bukatar Mutane Su Kula Da Warin Jikinsu

Bukatar Mutane Su Kula Da Warin Jikinsu

September 27, 2025
Me Ya Sa Kamfanonin Jamus Fiye Da 560 Suka Zabi Wani Gari A Kasar Sin Don Gudanar Da Harkokinsu?

Me Ya Sa Kamfanonin Jamus Fiye Da 560 Suka Zabi Wani Gari A Kasar Sin Don Gudanar Da Harkokinsu?

September 27, 2025
Matsalar Tasgadewar Kashin Baya

Matsalar Tasgadewar Kashin Baya

September 27, 2025
Firaministan Sin: Adalci Shi Ne Abu Mafi Daraja A Wurin Kasashen Duniya 

Firaministan Sin: Adalci Shi Ne Abu Mafi Daraja A Wurin Kasashen Duniya 

September 27, 2025
Yadda Ake Hada Sushi

Yadda Ake Hada Sushi

September 27, 2025
Ribar Da Manyan Kamfanonin Kasar Sin Ke Samu Ta Dawo Turbar Karuwa A Watanni 8 Na Farkon Bana

Ribar Da Manyan Kamfanonin Kasar Sin Ke Samu Ta Dawo Turbar Karuwa A Watanni 8 Na Farkon Bana

September 27, 2025
Atletico Madrid Ta Zazzaga Wa Real Madrid Ƙwallaye 5 A Metropolitano

Atletico Madrid Ta Zazzaga Wa Real Madrid Ƙwallaye 5 A Metropolitano

September 27, 2025
Tawagar Gwamnatin Tsakiya Na Ci Gaba Da Ziyartar Jami’ai Da Mazauna Yankuna Da Dama Na Jihar Xinjiang

Tawagar Gwamnatin Tsakiya Na Ci Gaba Da Ziyartar Jami’ai Da Mazauna Yankuna Da Dama Na Jihar Xinjiang

September 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.