• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
24 hours ago
in Manyan Labarai, Addini
0
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Idan aka ce Tsayuwar Arfa, ba ana nufin mutum ya yi ta tsayawa ne kyam, babu zama, babu hutawa, babu kwanciya ba, a’a, ko mutum barci yake yi a filin Arfa to yana daga cikin tsayuwar Arfan.

An karɓo Hadisi daga Jabir (RA) Annabi (SAW) ya ce “Babu wasu kwanaki masu daraja da girma a wajen Allah da suka fi kwana goma nan na farkon watan Sallar Layya”.

  • Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfah
  • Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

A cikin kwanakin ne ake hawa Arfa a ranar 9 ga wata, ranar 10 ga wata ake gudanar da sauran manyan ayyukan Hajji irin su Jifa, Hadaya, Aski da ɗawaful Ifada. Kuma a rannan ne sauran Musulmi a duk inda suke a duniya suke yin Sallar Idi da taya Alhazai yanka da liyafar taya su murnar sun yi Hajji lafiya.

Wasu Malamai sun yi bayanin cewa hatta kwana 10 na ƙarshen watan Ramadan ba su kai waɗannan kwanaki goman ba. Shi ya sa yin azumi a cikinsu ga wanda ba ya Aikin Hajji, da yin nafilfilin dare suke da ɗimbin falala.

Wani mutum ya tambayi Annabi (SAW) cewa “Kwana 10 ɗin nan sun fi hatta yaƙin tsayar da Tafarkin Allah da ake cewa wanda ya mutu a ciki ɗan Aljanna ne, wanda ya dawo – da rai – zai dawo da lada mai yawa?”. Annabi (SAW) ya ce “Eh, sun fi yaƙin tsayar da Tafarkin Allah.”

Labarai Masu Nasaba

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

Sannan Annabi (SAW) ya ce “Babu wata rana mafificiya a wajen Allah kamar Ranar Arfa”, haka nan kuma ragowar kwanakin da ke cikin 10 na farkon watan nan, Ranar Arfa ta ninninka su falala. Don a wannan ranar ce Annabi (SAW) ya ce Ubangiji yana sauka zuwa saman duniya (Kamar yadda ya dace da Shi (SWT). Ire-iren waɗannan Hadisan ne ake ce musu “Mutashabihai”. Ana kawo bayanansu ne ta yadda za a yi mana kwatance amma ba kamar yadda ma’anar lamarin yake a hulɗar da ke tsakaninmu ba.
Wajibi ne yin imani da Hadisan don rashin yin imani da su ridda ne, amma ba kuma a riƙa fassarawa da yadda ƙananan ƙwaƙwalenmu ke ɗaukawa ba. Duk wanda ya ce zai fassara da ƙaramin hankalinsa, to wannan ya sa wasa a cikin sha’anin Allah (SWT).
Hadisin ya ci gaba da cewa “Ubangiji yana sauka a saman duniya sai ya yi alfahari da mutanen doron ƙasa. Yana kallon mutanen yana wa Mala’iku alfahari da su cewa ku kalli bayina, sun zo mun da birkitaccen gashi masu ƙura-ƙura, ga su sun yini, sun zo mun daga nesan duniya suna neman rahamata, ba su ga azabata ba.” Munzir ya ce Abu Ya’ala, Bazzaru, Ibn Khuzaima da Ibn Hibban suka ruwaito Hadisin. Amma lafazin da aka ruwaito da shi kuwa, na Ibn Mubarak ne daga Safyanus Sauri, shi kuma daga Zubairu bin Aliyin daga Anas bin Malik (RA).

Ma’anar kai ya yi ƙura-ƙura, ko da gashin mutum bai yi ƙura ba, Allah zai ba shi ladan, shi dai ya kasance ya kiyaye abubuwan da Shari’a ta ce ma sa kar ya yi. A kan haka ne ya sa ba a so a riƙa yin kwalliya bayan wanda aka yi a yayin ɗaukan harami.

Annabi (SAW) ya ce ba a taɓa ganin wata ranar da ake ‘yantar da bayi daga barin shiga wuta kamar Ranar Arfa ba. Duk zunubin da aka yi a shekara, rannan Allah yana zubar da shi.

  • Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji

An karɓo kuma daga Ibn Mubarak, daga Safyanus Sauri, daga Zubairu bin Aliyin, shi kuma daga Anas bin Malik (RA) ya ce, “Annabi (SAW) ya tsaya a Arfa, da rana ta kusa faɗuwa, sai Annabi ya kira Bilalu ya ce ya sa mutane su yi shiru zai yi magana, sai Bilalu ya tashi ya ce wa jama’a; ku yi shiru ga Annabi (SAW). Sai Annabi (SAW) ya tashi yana kan raƙumi ya ce, “Ya ku taron mutane, yanzu Jibrilu ya zo mun ya gaishe ni, ya ce Ubangijina ya gafarta wa duk waɗanda suka zo Arfa ɗin nan, da waɗanda duk suka zo Mina (Mash’aril Harami) kuma Allah ya lamunce musu duk laifin da ke kansu”. Sai Sayyidina Umar bin Khaɗɗab (RA) ya miƙe ya ce “Ya Ma’aikin Allah, wannan namu ne da muka zo wannan Hajjin kawai? Sai Annabi (SAW) ya amsa ma sa da cewa “Naku ne kuma da duk waɗanda za su zo Arfa a bayanku har tashin ƙiyama”. Sai Sayyidina Umar (RA) ya ce “Alherin Allah yana da yawa kuma ya yi daɗi”. Imam Muslim da waninsa suka ruwaito.

Har ila yau, an karɓo wani Hadisin daga Ummul Mu’umina Aisha (RA) cewa Manzon Allah (SAW) ya ce, “Babu wata rana da Allah yake yawaita ‘yanta bayinsa daga wuta kamar Ranar Arfa. Ubangiji yana kusantowa (SWT) ga mutane har ya yi wa Mala’iku alfahari da su ya ce, “Me waɗannan mutane suke so ne?”.

Wannan yana nuna tambayar ta jindaɗi ce (yadda ya dace da Allah), saboda ai ya san abin da kowa yake so amma kuma sai ga shi (SWT) yana tambayar Mala’iku. Haƙiƙa ba ƙaramar falala ba ce a ce Allah ya yi alfahari da mutum, Alhamdu Lillah.

An karɓo Hadisi daga Abu Darda’i (RA) cewa Annabi (SAW) ya ce, “Babu wata rana da ake ganin Shaiɗan a matsayin mafi ƙasƙanci da wulaƙanta da tunkuɗewa da fushi kamar Ranar Arfa”. Ba komai ya jawo ma sa wannan ba sai abin da yake gani na Rahamar Allah da take sauka.

Hatta shi kansa Shaiɗan yana zuwa Arfa, a maimakon shi ma ya samu yafiya a wurin Allah, sai kuma ya sake jibgan wani laifin saboda hassada a kan Rahamar da Allah yake wa bayinsa. Yana-ji-yana-gani, Allah zai yafe wa al’umma duk saɓon da ya ingiza su suka aikata.

Wannan baƙin cikin ma bai isa ba, tun da har ya yi hassada, ya ji baƙin cikin gafarar da Allah ya yi wa bayinsa, za a kuma tafi Mina bayan an sauko daga Arfa a jefe shi a can.
Ko kuma dama shi duk mai hassada idan ya ga wanda Allah ya baiwa ni’imar da yake baƙin ciki a kai; sai ya ji rashin lafiya ta taso ma sa. Abin da yake samun Iblis kenan. Al’umma za su taso daga Arfa cikin gafara kuma su je su jefe shi.

Haka nan, ya yi irin wannan baƙin cikin Ranar Badar. Da aka tambayi Annabi (SAW) irin baƙin cikin da ya yi a ranar, Annabi (SAW) ya ce “Iblis da ya ga Jibrilu yana jagorantar Rundunar Mala’iku, ba a taɓa ganin tsoro ya kama shi irin na rannan ba, har ma ya mance ya ce yana tsoron Allah”.

Allah ya amfanar da mu baki ɗaya, Albarkar Annabi (SAW).


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArfaHajjiIbadaKasa Mai TsarkiMadinaMakkahManzon AllahSalatiZakiri
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

Next Post

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

Related

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

30 minutes ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 hour ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

15 hours ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

21 hours ago
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja
Manyan Labarai

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

22 hours ago
Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa
Manyan Labarai

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

1 day ago
Next Post
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

June 6, 2025
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

June 6, 2025
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 6, 2025
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.