• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin Bana: Ku Zama Jakadu Na Kwarai – Gwamnan Gombe Ga Maniyyata

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Hajjin Bana: Ku Zama Jakadu Na Kwarai – Gwamnan Gombe Ga Maniyyata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bukaci maniyyatan jihar zuwa Saudiyya su kasance masu biyayya da bin doka da oda, kuma su kasance jakadu na gari ga jihar da Nijeriya a yayin da suke ƙkasa mai tsarki. 

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne a jiya yayin jawabin sa na bankwana ga maniyyatan jihar a hukumar jin dadin alhazai ta Jihar Gombe, “Yayin da kuke kasa mai tsarki, don Allah ku kasance jakadu nagari ga kanku, da al’ummarku, da kananan hukumominku, da Jihar Gombe dama Nijeriya, don mu yi alfahari da ku,” in ji shi.

  • Hajjin Bana: Kashin Farko Na Maniyyatan Adamawa 475 Sun Sauka Saudiyya

Da yake kira ga maniyyatan su nesanta kansu daga duk wani abu da ka iya bata musu aikin na Hajji, ko taba mutuncin su ko na Jihar Gombe, Gwamna Inuwa ya tunatar da su cewa a kasa mai tsarki doka tana aiki ba sani ba sabo kan duk wadda aka kama da aikata laifi ko rashin gaskiya.

 

Labarai Masu Nasaba

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Da yake yi wa maniyyatan fatan gudanar da karbabben aikin Hajji, gwamnan ya karfafa su da su rika tambayar jagororinsu kan duk wani abu da ya shige mu su duhu. Ya ce gwamnatinsa ta himmatu wajen ganin alhazan jihar sun yi aikin Hajji cikin natsuwa tun daga Nijeriya har zuwa kasa mai tsarki.

Hajjin Bana

Da yake tsokaci kan matsalolin rayuwa dana tattalin arziki da zamantakewar al’ummar kasar nan, Gwamna Inuwa Yahaya ya buƙaci maniyatan su zage damtse wajen yin addu’o’in Allah ya samar wa kasar mafita.

 

Gwamnan ya kuma bukaci jami’an hukumomin alhazai a dukkan matakai su gudanar da ayyukan su cikin gaskiya da amana da kishin kasa don gudanar da aikin Hajjin cikin nasara.

 

A nasa jawabin, Shugaban Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Gombe, Mai Martaba Sarkin Dukku, Haruna Abdulkadir Rasheed, ya yaba wa gwamnan bisa jajircewarsa na ganin an gudanar da aikin Hajji na bana cikin nasara.

 

Da yake jan hankalin alhazan jihar su maida hankali ga ibada maimakon sayen tsaraba, shugaban ya bukaci maniyyatan su ba da hadin kai ga jami’an aikin Hajji na jiha da na kasa don samun nasarar gudanar da aikin.

Hajjin Bana

A jawabinsa na maraba, babban sakataren hukumar Alhaji Sa’adu Hassan, ya yaba wa gwamnan bisa samar da ingantaccen masauki ga maniyyatan jihar a ƙasa mai tsarki.

 

Ya ce da farko jirgi mai daukar alhazai 350 aka tsara zai yi jigilar alhazan jihar, amma bisa jajircewar da gwamnan ya yi, yanzu an samar da jirgi mai daukan mutum 550 da zai tashi da sawun farko na maniyyatan jihar. Ya ce bayan tantance maniyyatan da aka lika sunayensu, za a fara jigilar mahajjatan gadan-gadan a gobe Laraba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zuba Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Da Japan Ke Shirin Yi Zai Illata Duk Fadin Duniya

Next Post

Gwamnoni Sun Mara Wa Matakin Tinubu Na Cire Tallafin Mai Baya

Related

Ministan Tsaro
Labarai

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

55 minutes ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 hour ago
Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya
Labarai

Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

3 hours ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

3 hours ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

4 hours ago
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano
Labarai

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

13 hours ago
Next Post
Gwamnoni Sun Mara Wa Matakin Tinubu Na Cire Tallafin Mai Baya

Gwamnoni Sun Mara Wa Matakin Tinubu Na Cire Tallafin Mai Baya

LABARAI MASU NASABA

Ministan Tsaro

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

June 6, 2025
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

June 6, 2025
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

June 6, 2025
Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

June 6, 2025
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

June 6, 2025
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 6, 2025
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.