ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin Bana: Ku Zama Jakadu Na Kwarai – Gwamnan Gombe Ga Maniyyata

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Hajjin Bana

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bukaci maniyyatan jihar zuwa Saudiyya su kasance masu biyayya da bin doka da oda, kuma su kasance jakadu na gari ga jihar da Nijeriya a yayin da suke ƙkasa mai tsarki. 

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne a jiya yayin jawabin sa na bankwana ga maniyyatan jihar a hukumar jin dadin alhazai ta Jihar Gombe, “Yayin da kuke kasa mai tsarki, don Allah ku kasance jakadu nagari ga kanku, da al’ummarku, da kananan hukumominku, da Jihar Gombe dama Nijeriya, don mu yi alfahari da ku,” in ji shi.

ADVERTISEMENT
  • Hajjin Bana: Kashin Farko Na Maniyyatan Adamawa 475 Sun Sauka Saudiyya

Da yake kira ga maniyyatan su nesanta kansu daga duk wani abu da ka iya bata musu aikin na Hajji, ko taba mutuncin su ko na Jihar Gombe, Gwamna Inuwa ya tunatar da su cewa a kasa mai tsarki doka tana aiki ba sani ba sabo kan duk wadda aka kama da aikata laifi ko rashin gaskiya.

 

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

Da yake yi wa maniyyatan fatan gudanar da karbabben aikin Hajji, gwamnan ya karfafa su da su rika tambayar jagororinsu kan duk wani abu da ya shige mu su duhu. Ya ce gwamnatinsa ta himmatu wajen ganin alhazan jihar sun yi aikin Hajji cikin natsuwa tun daga Nijeriya har zuwa kasa mai tsarki.

Hajjin Bana

Da yake tsokaci kan matsalolin rayuwa dana tattalin arziki da zamantakewar al’ummar kasar nan, Gwamna Inuwa Yahaya ya buƙaci maniyatan su zage damtse wajen yin addu’o’in Allah ya samar wa kasar mafita.

 

Gwamnan ya kuma bukaci jami’an hukumomin alhazai a dukkan matakai su gudanar da ayyukan su cikin gaskiya da amana da kishin kasa don gudanar da aikin Hajjin cikin nasara.

 

A nasa jawabin, Shugaban Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Gombe, Mai Martaba Sarkin Dukku, Haruna Abdulkadir Rasheed, ya yaba wa gwamnan bisa jajircewarsa na ganin an gudanar da aikin Hajji na bana cikin nasara.

 

Da yake jan hankalin alhazan jihar su maida hankali ga ibada maimakon sayen tsaraba, shugaban ya bukaci maniyyatan su ba da hadin kai ga jami’an aikin Hajji na jiha da na kasa don samun nasarar gudanar da aikin.

Hajjin Bana

A jawabinsa na maraba, babban sakataren hukumar Alhaji Sa’adu Hassan, ya yaba wa gwamnan bisa samar da ingantaccen masauki ga maniyyatan jihar a ƙasa mai tsarki.

 

Ya ce da farko jirgi mai daukar alhazai 350 aka tsara zai yi jigilar alhazan jihar, amma bisa jajircewar da gwamnan ya yi, yanzu an samar da jirgi mai daukan mutum 550 da zai tashi da sawun farko na maniyyatan jihar. Ya ce bayan tantance maniyyatan da aka lika sunayensu, za a fara jigilar mahajjatan gadan-gadan a gobe Laraba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC
Manyan Labarai

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama
Manyan Labarai

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

November 15, 2025
Next Post
Gwamnoni Sun Mara Wa Matakin Tinubu Na Cire Tallafin Mai Baya

Gwamnoni Sun Mara Wa Matakin Tinubu Na Cire Tallafin Mai Baya

LABARAI MASU NASABA

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

November 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

November 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.