• English
  • Business News
Thursday, July 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin Bana: NAHCON Za Ta Fara Jigilar Maniyyata A Ranar 6 Ga Mayu

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
4 months ago
in Labarai
0
hajjin 2024
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kula da jin dadin da alhazai ta Nijeriya (NAHCON) ta ware ranar 6 ga watan Mayu domin fara jigilar maniyyata daga nan gida Nijeriya zuwa kasa mai tsarki ga wadanda za su sauke farali a shekarar 2025.

Da yake magana a yayin sanya hannun yarjejeniya da zababbun kamfanonin jiragen da za su yi aikin jigilar maniyyata a ranar Litinin a Abuja, Kwamishinan ayyuka, bin sawu da lasisi na NAHCON, Prince Anofi Elegushi, ya ce, wannan na daga cikin shirye-shiryen da kamfanonin jiragen ke da shi domin jigilar maniyyatan Nijeriya.

  • Wata Rana Za A Yi Wa Gwamnatin Tinubu Sambarka – Minista 
  • Hadin Gwiwa Karkashin BRI Mai Inganci Na Ingiza Ci Gaban Duniya

Idan za a iya tunawa dai hukumar NAHCON ta sanar da cewa kamfanonin jiragen Mad Air, Air Peace, UMZA Airline da FlyNas ne aka zaba domin jigilar adadin maniyyata 52,000 da aka amince wa Nijeriya.

Elegushi ya bukaci kamfanonin jiragen saman da su yi duk mai yiyuwa wajen tabbatar da sun yi aiki mai inganci domin samun gudanar da jigilar cikin nasara da kwanciyar hankali.

Ya ce a wannan shekarar za su ga an biya su kudin kwantiraginsu cikin gaggawa, amma hakan zai kasan biya kan naira a jigilar daga Nijeriya da kuma biya kan Riyal na Saudi a yayin kwasowa daga Saudiya.

Labarai Masu Nasaba

Yawan Ma’aikata Ne Ya Hana Borno Fara Biyan Sabon Mafi Ƙarancin Albashi – Zulum

EFCC Ta Kama Ɗaliban BUK 25 Kan Zargin Aikata Damfara A Intanet A Kano

“Muna kokarin kawar da bangaren dala. Abin da muke so mu yi shi ne mu biya a cikin kudin gida na duk kamfanonin jiragen sama. Kuma za a biya kudin ne daidai da farashin dala a halin yanzu a lokacin da ake biya.
“Kason da ya dace ya ba ku damar gudanar da ayyukanku dukkan ne za a biya ku, bayan kammala aikin za a karasa biyanku sauran,” ya shaida.

Tun da farko, shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Usman Saleh, ya ce, ayyukan jirage na sufuri na daga cikin muhimman ayyukan da ke gabansu wajen sauke nauyin aikin hajji.
“Lamarin na bukatar kwarewa matuka gaya da kuma himma da azama. Wannan lamarin ba kawai ga batun sufuri ba ne, ya shafi har da ciki alkawuran da aka dauka da mutuntaka da kariya hadi da saukaka wa maniyyata.”

Ya ce kamfanonin jiragen sama da aka yi aikin sun gudanar da cikakken tsarin zabe bisa cancanta, amintacce da kuma ingantaccen aiki.

“NAHCON ta yi taka-tsan-tsan wajen tabbatar da cewa kamfanonin jiragen sama masu inganci, ingantattun kayan aiki da fasinja ne kadai aka damka wa wannan gagarumin aiki.
“Kwarewarku da tarihinku na gudanar da manyan ayyuka, musamman ayyukan da suka shafi aikin hajji, sun ba mu kwarin gwiwa kan iyawar ku na gudanar da jigilar hajji cikin sauki.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wata Rana Za A Yi Wa Gwamnatin Tinubu Sambarka – Minista 

Next Post

Gidauniyar Dangote Ta Kaddamar Da Rabon Abinci Na Naira Biliyan 16 Ga Talakawan Nijeriya

Related

Yawan Ma’aikata Ne Ya Hana Borno Fara Biyan Sabon Mafi Ƙarancin Albashi – Zulum
Labarai

Yawan Ma’aikata Ne Ya Hana Borno Fara Biyan Sabon Mafi Ƙarancin Albashi – Zulum

2 hours ago
EFCC Ta Kama Ɗaliban BUK 25 Kan Zargin Aikata Damfara A Intanet A Kano
Labarai

EFCC Ta Kama Ɗaliban BUK 25 Kan Zargin Aikata Damfara A Intanet A Kano

3 hours ago
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato
Labarai

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 11 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Sakkwato

4 hours ago
Sojoji Sun Kwato Makamai Da Babura, Sun Ceto Mutane 3 A Kaduna 
Manyan Labarai

Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Bindiga Sama Da 100 A Neja

5 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Sake Ciyo Bashin Dala Biliyan 21 Daga Ƙetare

6 hours ago
Sojoji Sun Kashe Kwamandan Boko Haram A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Boko Haram A Borno

14 hours ago
Next Post
Gidauniyar Dangote Ta Kaddamar Da Rabon Abinci Na Naira Biliyan 16 Ga Talakawan Nijeriya

Gidauniyar Dangote Ta Kaddamar Da Rabon Abinci Na Naira Biliyan 16 Ga Talakawan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Ministan Lafiya Na Kamaru: Hadin-Gwiwa Ta Fuskar Kiwon Lafiya Ta Shaida Zumunci Mai Karfi Tsakanin Kamaru Da Sin

Ministan Lafiya Na Kamaru: Hadin-Gwiwa Ta Fuskar Kiwon Lafiya Ta Shaida Zumunci Mai Karfi Tsakanin Kamaru Da Sin

July 24, 2025
Yawan Ma’aikata Ne Ya Hana Borno Fara Biyan Sabon Mafi Ƙarancin Albashi – Zulum

Yawan Ma’aikata Ne Ya Hana Borno Fara Biyan Sabon Mafi Ƙarancin Albashi – Zulum

July 24, 2025
EFCC Ta Kama Ɗaliban BUK 25 Kan Zargin Aikata Damfara A Intanet A Kano

EFCC Ta Kama Ɗaliban BUK 25 Kan Zargin Aikata Damfara A Intanet A Kano

July 24, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 11 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Sakkwato

July 24, 2025
Sojoji Sun Kwato Makamai Da Babura, Sun Ceto Mutane 3 A Kaduna 

Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Bindiga Sama Da 100 A Neja

July 24, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Sake Ciyo Bashin Dala Biliyan 21 Daga Ƙetare

July 24, 2025
Sojoji Sun Kashe Kwamandan Boko Haram A Borno

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Boko Haram A Borno

July 24, 2025
An Kaddamar Da Bikin BIRTV2025 A Beijing

An Kaddamar Da Bikin BIRTV2025 A Beijing

July 23, 2025
Tinubu Ya Tattauna da Gwamnonin APC Kafin Muhimmin Taron NEC

Tinubu Ya Tattauna da Gwamnonin APC Kafin Muhimmin Taron NEC

July 23, 2025
Masu Zuba Jari Na Kasa Da Kasa Sun Gamsu Zuba Jari A Sin Dama Ce Ta Cimma Nasarar More Riba A Nan Gaba

Masu Zuba Jari Na Kasa Da Kasa Sun Gamsu Zuba Jari A Sin Dama Ce Ta Cimma Nasarar More Riba A Nan Gaba

July 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.