• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Halin Maza Muke Rubutawa, Ba Wai Sharri Muke Musu Ba – Amina Ma’aji

by Leadership Hausa
1 year ago
in Adon Gari
0
Halin Maza Muke Rubutawa, Ba Wai Sharri Muke Musu Ba – Amina Ma’aji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Marubuciyar yanar gizo, da ita ma take kan ganiyarta AMINA MA’AJI ta yi ikirarin cewa ko daya ba sa wa maza wani zambo ko habaici a cikin rubuce-rubucensu face gaskiyar halayen mazan da suke fada a inda ta kama. Ga dai tattaunawarsu da ADAMU YUSUF INDABO kamar haka:

Wace ce Amina Ma’aji?
Assalamu Alaikum. Cikakken sunana ke nan Amina maaji, wanda aka fi sani da Maman Khairat. Ni y’ar jahar Yobe ne a Potiskuma, nan aka haife ni na yi rayuwa, nan na yi karatu tun daga kan primary har i zuwa makarantan hurar da malamai ‘Federal College Of Education (Technical) Potiskum’ inda na karanci mathematics and computer, na gama a shekarar 2015. Yanzu haka kuma ina aure ne a garin Damaturu. Ina da yara guda hudu maza biyu mata biyu.

A duniyar rubutu mun san wata marubuciya Ummi Ma’aji, sai kuma ga Amina Ma’aji ta bayyana. To mene alakarki da ita?
Sunane kawai ya zo daya, amma Ummi Ma’aji bana da alaka ta jini da ita face ta musulunci, sai ta rubutu, kuma daya daga cikin gwanayen marubutana, so na dade da sanin ta, kuma ina bukatan haduwa da ita. Amma har yanzu Allah bai kaddara haduwarmu ba.

To mene tarihin kasantuwar ki a cikin duniyar rubutu?
Tun farko ni mai son karance-karance ne, tun ina Jss 2 nake son karatu nakan dauki takaddata in ta rubuta labari sosai, da na je ss 1 ni ce mai karanta littafi a mutane da labari mai dadi. Yayin da na gama makaranta, sai karatun ya shiga raina, mahaifiya ta takan ba ni kudi in siyo littafi dan in karanta. Na fara karanta littafin Hadiza Salisu shareef ‘SO’ ya yi mun dadi sosai na samu darasi a cikin littafin, darusa kuma masu yawan gaske. Allah Ya ji kan ta Amin. Daga sai na zama mai karance-karance da yawa. Akwai wata marubuciya Sa’adatu Wazeeri Gombe ita ce ta fara ba ni shawara in yi rubutu dan ta ga ina da fahimtar abu da wuri. Na ce mata babu kudi. To shi ne na tambayi wani ana ce mishi Adamu dan tare muke karatu, yace in fara na tambayi kanina Musaddam shi ya fara ba ni goyon baya na rubuta littafina na farko ‘Namiji Karin Kunama’ na sha wahala wajen rubutawa saboda rashin sabo labarin cikin littafin, labarina ne na kaina. Amma a halin yanzu rubutu ya zame mini abunda ke sa ni farin ciki.

Ke nan Namiji Karin Kunama ne littafi na farko da kika rubutawa?
Kwarai, Shi ne littafina na farko a duniyan rubutu. Na rubutu ahi a karshen shekaran 2015. Daga shi ban sake littafi ba sai 2016.

Labarai Masu Nasaba

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

Sunan littafin Namiji Karin Kunama, ya tabbatar da zargin da ake cewa littafan Marubuta mata, yawancinsu zambo ne da habaici wa maza. Wai me yake kawo haka?
To gaskiya ni dai bana rubuta littafin da bai faru da gaske, ba wasu hakan ne za su hanga a mahangarsu. Amma ni ai tarihin rayuwata ne na bayar a cikin littafin ‘Namiji Karin Kunama’ lokacin da na fada SO mai wuyar fassara, su mazan sun yi abun rubutun ne yawanci in ka ga mace ta yi rubutu a kan maza, daman can halinsu ne babu sharri. Allah ya sa mu dace. Kuma mu ma matan In labarin ya juyo gare mu mukan iya rubutawa. Kuma littafin ya yi duba ne ga maza masu janyewa daga masu yi musu halacci, ya yi duba a kan zurfafa soyayya daga karshe su wufce subar mutum da hamma, a kwai yaudara da cin mutunci ha’i ci, aikin da na sani.

Ya yi duba ne ga samari da ba su da komai mace takan zama da su a haka daga baya, in wadata ya zo musu ka neme su ka rasa su, kun sha wahala tare kudi ba tare da ku za a ci ba. To ka ga wannan duk halin maza ne, sai illa nadiran.

Za mu ci gaba makon gobe


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Halin MazaRayuwar 'yanmata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nathan Tella: Matashin Da Ke Fatan Buga Wa Nijeriya Wasa

Next Post

Dan Majalisar Amurka Ya Yi Wa Takwaransa Mahangurba

Related

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

2 weeks ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

3 months ago
Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar
Adon Gari

Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar

4 months ago
Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam
Adon Gari

Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam

5 months ago
Nijeriya Da Brazil Sun Cimma Yarjejeniyar Bunkasa Noman Zamani A Kasar Nan
Adon Gari

Halima Aliko Dangote Ta Nemi A Ba Mata Damar Shiga Harkokin Kasuwanci Yadda Ya Kamata

5 months ago
Mata A Dage Da Karatu Yin Haka Taimakon Kanku Ne Da ‘Ya’yanku – Zainab Ahmad
Adon Gari

Mata A Dage Da Karatu Yin Haka Taimakon Kanku Ne Da ‘Ya’yanku – Zainab Ahmad

6 months ago
Next Post
Dan Majalisar Amurka Ya Yi Wa Takwaransa Mahangurba

Dan Majalisar Amurka Ya Yi Wa Takwaransa Mahangurba

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don YaÆ™ar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.