• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Ba Labari: Awanni 48 Bayan Sace Ƴan Jarida Da Iyalansu A Kaduna

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Labarai, Manyan Labarai
0
Har Yanzu Ba Labari: Awanni 48 Bayan Sace Ƴan Jarida Da Iyalansu A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Awanni 48 bayan sace ƴan jarida biyu da iyalansu a Jihar Kaduna, har yanzu ba a san inda suke ba. ‘Yan bindiga sun kutsa cikin unguwar Danhonu a Millennium City, ƙaramar hukumar Chikun, inda suka kai hari gidajen AbdulGafar Alabelewe na jaridar The Nation da AbdulRaheem Aodu na jaridar Blueprint, suka sace su tare da matansu da ‘ya’yansu. An sako matar AbdulRaheem daga baya saboda rashin iya bin masu sacewa sakamakon rashin lafiya.

Ɗan uwa ga ɗaya daga cikin waɗanda aka sace, Taofeeq Olayemi, ya bayyana damuwar da iyalan suke ciki, yana mai cewa ba su samu wata alaƙa da ‘yan uwan da aka sace ba tun bayan faruwar lamarin ba. Ya ce, “Wannan lokaci ne mai matuƙar wahala ga iyalan saboda ba mu san halin da suke ciki ba kuma ba mu san inda suke ba. Muna ta addu’a ga Allah ya kiyaye su kuma ya sassauta zuciyar waɗanda suka sace su.”

  • Ƴancin Ƙananan Hukumomi Zai Taimaka Wajen Magance Matsalolin Tsaro – COAS
  • Atiku Ya Koka Kan Yadda Matsalar Tsaro Ta Addabi ‘Yan Nijeriya

Kakakin rundunar ‘yan sanda (PPRO) a Kaduna, ASP Mansir Hassan, ya ce jami’an tsaro suna iyakar kokarinsu don ganin sun kuɓutar da waɗanda aka sace ba tare da wani rauni ba. Ya bayyana cewa an tura jami’ai cikin dajin da ake zaton ‘yan bindigar suke buya.

Ƙungiyar ‘Yan Jaridu ta Najeriya (NUJ) a Kaduna ta yi tir da wannan sacewa a cikin wata sanarwa da shugaban ƙungiyar, Comrade Asmau Yawo Halilu, da Sakataren ƙungiyar, Comrade Gambo Santos Sanga, suka sanya wa hannu. Sun roƙi hukumomin tsaro da su ɗauki matakin gaggawa don ceto ‘yan jaridar da iyalansu.

Kungiyar Arewa Youth Consultative Forum (AYCF) ta yi Allah wadai da garkuwar da aka yi da ƴan jaridar. Shugaban ƙungiyar, Alhaji Yerima Shettima, ya yi kira ga hukumomin gwamnati da na tsaro su ƙara kokari don ganin an sako waɗanda aka sace lafiya kuma a kawo karshen irin waɗannan munanan al’amura. Ya kuma bukaci jama’a su yi addu’a don ganin an sako waɗanda aka sace lafiya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Uba Sani Ya Buƙaci Al’ummar Jihar Kaduna Da Su Yi Rijistar Katin Zaɓe 

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BanditsJournalismJournalistKidnappersNewsRadioTelevisionTerrorist
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Gana Da Firaministan Hungary

Next Post

Ba Samar Da Damar Samun Ci Gaba Kawai Ke Sa Kasar Sin Samun Karbuwa Ba

Related

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Manyan Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Buƙaci Al’ummar Jihar Kaduna Da Su Yi Rijistar Katin Zaɓe 

59 minutes ago
DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu
Manyan Labarai

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

3 hours ago
PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu
Manyan Labarai

PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

4 hours ago
Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME
Ilimi

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

5 hours ago
Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja
Kiwon Lafiya

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

6 hours ago
Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida
Manyan Labarai

Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

7 hours ago
Next Post
Ba Samar Da Damar Samun Ci Gaba Kawai Ke Sa Kasar Sin Samun Karbuwa Ba

Ba Samar Da Damar Samun Ci Gaba Kawai Ke Sa Kasar Sin Samun Karbuwa Ba

LABARAI MASU NASABA

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Buƙaci Al’ummar Jihar Kaduna Da Su Yi Rijistar Katin Zaɓe 

September 8, 2025
Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

September 8, 2025
DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

September 8, 2025
PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

September 8, 2025
Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

September 8, 2025
Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

September 8, 2025
Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

September 8, 2025
Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.