• English
  • Business News
Friday, June 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Ba Labari: Awanni 48 Bayan Sace Ƴan Jarida Da Iyalansu A Kaduna

by Abubakar Sulaiman
12 months ago
in Labarai, Manyan Labarai
0
Har Yanzu Ba Labari: Awanni 48 Bayan Sace Ƴan Jarida Da Iyalansu A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Awanni 48 bayan sace ƴan jarida biyu da iyalansu a Jihar Kaduna, har yanzu ba a san inda suke ba. ‘Yan bindiga sun kutsa cikin unguwar Danhonu a Millennium City, ƙaramar hukumar Chikun, inda suka kai hari gidajen AbdulGafar Alabelewe na jaridar The Nation da AbdulRaheem Aodu na jaridar Blueprint, suka sace su tare da matansu da ‘ya’yansu. An sako matar AbdulRaheem daga baya saboda rashin iya bin masu sacewa sakamakon rashin lafiya.

Ɗan uwa ga ɗaya daga cikin waɗanda aka sace, Taofeeq Olayemi, ya bayyana damuwar da iyalan suke ciki, yana mai cewa ba su samu wata alaƙa da ‘yan uwan da aka sace ba tun bayan faruwar lamarin ba. Ya ce, “Wannan lokaci ne mai matuƙar wahala ga iyalan saboda ba mu san halin da suke ciki ba kuma ba mu san inda suke ba. Muna ta addu’a ga Allah ya kiyaye su kuma ya sassauta zuciyar waɗanda suka sace su.”

  • Ƴancin Ƙananan Hukumomi Zai Taimaka Wajen Magance Matsalolin Tsaro – COAS
  • Atiku Ya Koka Kan Yadda Matsalar Tsaro Ta Addabi ‘Yan Nijeriya

Kakakin rundunar ‘yan sanda (PPRO) a Kaduna, ASP Mansir Hassan, ya ce jami’an tsaro suna iyakar kokarinsu don ganin sun kuɓutar da waɗanda aka sace ba tare da wani rauni ba. Ya bayyana cewa an tura jami’ai cikin dajin da ake zaton ‘yan bindigar suke buya.

Ƙungiyar ‘Yan Jaridu ta Najeriya (NUJ) a Kaduna ta yi tir da wannan sacewa a cikin wata sanarwa da shugaban ƙungiyar, Comrade Asmau Yawo Halilu, da Sakataren ƙungiyar, Comrade Gambo Santos Sanga, suka sanya wa hannu. Sun roƙi hukumomin tsaro da su ɗauki matakin gaggawa don ceto ‘yan jaridar da iyalansu.

Kungiyar Arewa Youth Consultative Forum (AYCF) ta yi Allah wadai da garkuwar da aka yi da ƴan jaridar. Shugaban ƙungiyar, Alhaji Yerima Shettima, ya yi kira ga hukumomin gwamnati da na tsaro su ƙara kokari don ganin an sako waɗanda aka sace lafiya kuma a kawo karshen irin waɗannan munanan al’amura. Ya kuma bukaci jama’a su yi addu’a don ganin an sako waɗanda aka sace lafiya.

Labarai Masu Nasaba

Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma

An Nemi A Kafa Dokar Ta-ɓaci Kan Masu Ƙwacen Waya


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BanditsJournalismJournalistKidnappersNewsRadioTelevisionTerrorist
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Gana Da Firaministan Hungary

Next Post

Ba Samar Da Damar Samun Ci Gaba Kawai Ke Sa Kasar Sin Samun Karbuwa Ba

Related

Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma
Manyan Labarai

Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma

26 minutes ago
An Nemi A Kafa Dokar Ta-ɓaci Kan Masu Ƙwacen Waya
Manyan Labarai

An Nemi A Kafa Dokar Ta-ɓaci Kan Masu Ƙwacen Waya

1 hour ago
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina
Tsaro

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina

2 hours ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

11 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

13 hours ago
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano
Labarai

NDLEA Ta Kai Samame Fitattun Wuraren Shaye-shaye, Ta Cafke Mutane 19 A Kano

13 hours ago
Next Post
Ba Samar Da Damar Samun Ci Gaba Kawai Ke Sa Kasar Sin Samun Karbuwa Ba

Ba Samar Da Damar Samun Ci Gaba Kawai Ke Sa Kasar Sin Samun Karbuwa Ba

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma

Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma

June 20, 2025
An Nemi A Kafa Dokar Ta-ɓaci Kan Masu Ƙwacen Waya

An Nemi A Kafa Dokar Ta-ɓaci Kan Masu Ƙwacen Waya

June 20, 2025
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina

June 20, 2025
Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya

Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya

June 20, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

June 19, 2025
An Bude Baje Kolin Kayayyakin Sin Da Kudancin Asiya Karo Na 9 A Kunming

An Bude Baje Kolin Kayayyakin Sin Da Kudancin Asiya Karo Na 9 A Kunming

June 19, 2025
Sin Za Ta Hanzarta Duba Bukatun Samun Lasisin Fitar Da Ma’adanan “Rare Earth” Zuwa Ketare

Sin Za Ta Hanzarta Duba Bukatun Samun Lasisin Fitar Da Ma’adanan “Rare Earth” Zuwa Ketare

June 19, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

June 19, 2025
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

NDLEA Ta Kai Samame Fitattun Wuraren Shaye-shaye, Ta Cafke Mutane 19 A Kano

June 19, 2025
Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho

Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho

June 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.