ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Ba Labari: Awanni 48 Bayan Sace Ƴan Jarida Da Iyalansu A Kaduna

by Abubakar Sulaiman
2 years ago
Labari

Awanni 48 bayan sace ƴan jarida biyu da iyalansu a Jihar Kaduna, har yanzu ba a san inda suke ba. ‘Yan bindiga sun kutsa cikin unguwar Danhonu a Millennium City, ƙaramar hukumar Chikun, inda suka kai hari gidajen AbdulGafar Alabelewe na jaridar The Nation da AbdulRaheem Aodu na jaridar Blueprint, suka sace su tare da matansu da ‘ya’yansu. An sako matar AbdulRaheem daga baya saboda rashin iya bin masu sacewa sakamakon rashin lafiya.

Ɗan uwa ga ɗaya daga cikin waɗanda aka sace, Taofeeq Olayemi, ya bayyana damuwar da iyalan suke ciki, yana mai cewa ba su samu wata alaƙa da ‘yan uwan da aka sace ba tun bayan faruwar lamarin ba. Ya ce, “Wannan lokaci ne mai matuƙar wahala ga iyalan saboda ba mu san halin da suke ciki ba kuma ba mu san inda suke ba. Muna ta addu’a ga Allah ya kiyaye su kuma ya sassauta zuciyar waɗanda suka sace su.”

  • Ƴancin Ƙananan Hukumomi Zai Taimaka Wajen Magance Matsalolin Tsaro – COAS
  • Atiku Ya Koka Kan Yadda Matsalar Tsaro Ta Addabi ‘Yan Nijeriya

Kakakin rundunar ‘yan sanda (PPRO) a Kaduna, ASP Mansir Hassan, ya ce jami’an tsaro suna iyakar kokarinsu don ganin sun kuɓutar da waɗanda aka sace ba tare da wani rauni ba. Ya bayyana cewa an tura jami’ai cikin dajin da ake zaton ‘yan bindigar suke buya.

ADVERTISEMENT

Ƙungiyar ‘Yan Jaridu ta Najeriya (NUJ) a Kaduna ta yi tir da wannan sacewa a cikin wata sanarwa da shugaban ƙungiyar, Comrade Asmau Yawo Halilu, da Sakataren ƙungiyar, Comrade Gambo Santos Sanga, suka sanya wa hannu. Sun roƙi hukumomin tsaro da su ɗauki matakin gaggawa don ceto ‘yan jaridar da iyalansu.

Kungiyar Arewa Youth Consultative Forum (AYCF) ta yi Allah wadai da garkuwar da aka yi da ƴan jaridar. Shugaban ƙungiyar, Alhaji Yerima Shettima, ya yi kira ga hukumomin gwamnati da na tsaro su ƙara kokari don ganin an sako waɗanda aka sace lafiya kuma a kawo karshen irin waɗannan munanan al’amura. Ya kuma bukaci jama’a su yi addu’a don ganin an sako waɗanda aka sace lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

Gwamnatin Jigawa Ta Ɗaga Mafi Ƙarancin Fansho Zuwa Naira 20,000

Labari
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata
  • Abubakar Sulaiman
    Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

MASU ALAKA

Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar
Labarai

Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

July 8, 2026
Dole Ne Mace Ta Gaya Wa Mijinta Gaskiya Domin Ranar Hisabi – Matar Gwamnan Jigawa
Manyan Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Ɗaga Mafi Ƙarancin Fansho Zuwa Naira 20,000

July 8, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Labarai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Next Post
Ba Samar Da Damar Samun Ci Gaba Kawai Ke Sa Kasar Sin Samun Karbuwa Ba

Ba Samar Da Damar Samun Ci Gaba Kawai Ke Sa Kasar Sin Samun Karbuwa Ba

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar

July 8, 2026
Dole Ne Mace Ta Gaya Wa Mijinta Gaskiya Domin Ranar Hisabi – Matar Gwamnan Jigawa

Gwamnatin Jigawa Ta Ɗaga Mafi Ƙarancin Fansho Zuwa Naira 20,000

July 8, 2026
Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.