Jam’iyyar NNPP karkashin jagorancin Dakta Ajuji Ahmed mai biyayya ga Dakta Rabiu Musa Kwankwaso sun bayyana cewa yar yanzu shugabancin NNPP na hannunsu duk da hukuncin da kotu ta yanke a baya-bayan nan dangane da rikicin shugabancin da ake fama da shi a jam’iyyar.
Tun bayan zaben 2023, jam’iyyar NNPP ta shiga cikin rudani kan shugabanci, inda bangarorin da ke hamayya da juna ke fafatawa kan yadda za su tafiyar da shugabancin jam’iyyar, alamomi da tsarin NNPP.
- Sin Ba Za Ta Razana Da Zuwan Yakin Cinikayya Ba
- UBEC Ta Yaba Wa Jigawa Kan Inganta Harkar Ilimi A Jihar
Rikicin dai ya haifar da ruDani a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar da magoya baya, musamman a Kano, inda a halin yanzu jam’iyyar NNPP ke rike da madafun iko a jihar.
Wata babbar kotu da ke da zama a Abuja ta yi watsi da karar da tsagin Kwankwaso ya shigar. Kotun ta kalubalanci sahihancin wani bangare karkashin jagorancin Dakta Boniface Aniebonam da shugaban jam’iyyar na kasa, Dakta Agbo Major, wanda shi ma ya yi ikirarin shi ne halastaccen shugabancin jam’iyyar.
Shari’ar da Dakta Ajuji Ahmed da wasu mutum 20 suka shigar, ta nemi a soke ikon kwamitin amintattu na NNPP da bangaren zartarwa da suka hada da sakataren jam’iyyar na kasa na daya bangaranci, Oginni Olaposi, mataimakin shugaban jam’iyyar, Cif Felid Chukwurah da kuma lauya, Tony Obioha.
Masu shigar da kara sun bukaci kotun da ta hana wadannan jami’an gudanarwa gudanar da taro, ko kuma jagorantar babban taron jam’iyyar na kasa, bisa hujjar cewa an kore su daga jam’iyyar NNPP.
Ko da yake, alkali mai shari’a Justice MA Hassan ya yanke hukuncin cewa kotun ba ta da hurumin sauraren karar, inda ya bayyana cewa rikicin cikin gida na jam’iyyar kotun ba ta da hurumin sauyaran karar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp