ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Tinubu Na Biyan Tallafin Mai Ta Bayan Fage – IMF

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
IMF

LABARAI MASU NASABA

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

ADVERTISEMENT

Asusun bayar da lamuni na duniya (IMF) ya bayyana cewa gwamnatin Nijeriya karkashin Shugabancin Bola Ahmed Tinubu tana bayar da tallafin man fetur ta bayan fage.

Idan dai za a iya tunawa tun a ranar 29 ga Mayun 2023 lokacin da Shugaban kasa Tinubu yake jawabinsa na farko ya bayyana cire tallafin man fetur, wanda hakan ya haddasa tsadar farashin kayayyaki a cikin kasar nan.

  • Nijeriya Za Ta Shawo Kan Ƙalubalen Da Take Fuskanta Nan Gaba Kaɗan – Ganduje
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Gwamnoni Kan Ƙalubalen Da Nijeriya Ke Fuskanta

Bayan wasu ‘yan makonni, Babban Bankin Nijeriya ya rushe tsarin canjin kudaden waje zuwa na bai daya tare da karya darajar naira, wanda hakan ya janyo darajar naira da karye.

A wannan makon ne IMF ya shawarci gwamnatin tarayyar Nijeriya kan ta cire tallafin mai da na wutar lantarki gaba daya.

Sai dai kuma wannan shawara ya hadu da suka a wurin wasu ‘yan Nijeriya wadanda suke ganin a halin yanzu ma ana farama da matsin rayuwa ballantana an sake cire tallafin mai da kuma na wutar lantarki, inda suke ganin cewa idan har gwamnati ta amince da wannan shawara, to za a shiga mawuyacin halin da ba a taba shiga a Nijeriya ba.

A kwanakin baya ne wasu rahotanni suka bayyana cewa an samu dogayen layuka a gidajen man fetur a wasu manyan buranin kasar nan, amma kuma kamfanin mai na kasa (NNPC) ya bayyana wa ‘yan kasar cewa akwai isasshen man fetur.

Bayan cire tallafin man fetura a watan Mayun 2023, farashin litar man fetur ta tashi daga naira 185 zuwa 400, yayin da daga baya a gidajen mai na NNPC ake sayar da shi kan naira 568, sauran gidajen man kuma ana  sayar da shi ne kan naira 600.

Gwamnati ta bayyana cewa farashin man zai ci gaba da sauyawa lokaci bayan lokaci bayan cire tallafin man, amma kuma litar man zai tsaya yadda yake duk da sauyawan farashin danyan mai a kasuwar duniya, wanda yake iya hawa da kuma sauka.

IMF ta ce muddin gwamnatin Tinubu ta ci gaba da biyan tallafin man fetura da na wutar lantarki, zai ci gaba da janyo hauhawar farashin kayayyaki da tsadar rayuwa.

Wani bincike ya tabbatar da cewa duk da irin ikirarin Shugaba Tinubu na cire tallafin man fetur, gwamnatin tarayya ta biya tallafin naira biliyan 169.4 a watan Agustan baya domin farashin litar man ya ci gaba da zama kan naira 620.

Sai dai kuma sau uku dillalan man fetur suna kara farashin litar a tsakanin watan Agusta zuwa Disambar 2023, inda lamarin ya tilasta musu sayar da litar man kan tsakanin naira 660 zuwa 670.

Amma gidajen mai na NNPC na ci gaba da sayar da litar man kan naira 617. Yayin da suka gidajen mai na ‘yan kasuwa har sun fara sayar da litar man kan naira 720 a wasu wurare.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule
Manyan Labarai

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna
Labarai

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 
Labarai

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Next Post
Dalilin Kotu Na Dakatar Da Yanke Hukunci Kan Karar Zaben Tinubu

Dattawan Arewa Za Su Gabatar Wa Tinubu Shawarwari Kan Tattalin Arziki Da Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
'yansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

November 12, 2025
Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

November 12, 2025
Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.