• English
  • Business News
Wednesday, May 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hare-haren ‘Yan Bindiga: Za Mu Raba Tallafi Ga Mutanen Da Abin Ya Shafa A Katsina – Ministar Jinkai

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Shirin Inganta Rayuwa: Gwamnatin Tarayya Za Ta Rabawa Matan Karkara Naira Dubu 20
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta fara tattara sunayen waɗanda hare-haren ‘yan ta’adda ya shafa a wasu ƙananan hukumomi a Katsina.

 

Aikin tantance sunayen wanda ake gudanarwa a ƙarƙashin Ma’aikatar Ayyukan Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa wadda Hajiya Sadiya Farouk ce Minista, zai ɗauki sunayen ne daga ƙananan hukumomi 11 domin su shiga cikin tsarin masu cin gajiyar shirye-shiryen da ma’aikatar ke samar wa marasa galihu a faɗin ƙasar nan.

  • ‘Yansanda Sun Harbe ‘Yan Bindiga 2 A Jihar Katsina

Jagorar tawagar da ma’aikatar ta tura Katsina domin wayar da kan jama’a dangane da shirin ce ta bayyana haka.

 

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Harbe Wani Ɗan Bindiga, Sun Ƙwato Makamai Bayan Artabu A Taraba

Wata Hajiya ‘Yar Nijeriya Mai Shekaru 75 Ta Rasu A Saudiyya Yayin Aikin Hajji

Nadia Muhammad ta ce, ”waɗanda hare-haren ‘yan bindiga ya shafa su na cikin wani halin da su ke matuƙar buƙatar samun tagomashin canjin rayuwa.”

 

Daga cikin tsare-tsaren da za a saka sunayen waɗanda za a tantance ɗin har da shirin bayar da tallafin kuɗaɗe ga marasa galihu, shirin bayar da jarin tallafawa domin a yi ƙananan sana’o’i, shirin N-Power, shirin ciyar da ɗalibai da sauran su.

 

Da ta ke jawabi, Funke Olatunji wadda ta wakilci Shugabar Sashen Ayyukan Musamman a ma’aikatar, wato Nadia Muhammad, ta ce matsalar tsaro ta kawo cikas sosai wajen kasa kai kayan agaji da gudanar da ayyukan jinƙai a wasu yankunan karkarar da ‘yan bindiga su ka addabi jama’a da dama.

 

“Dalilin haka ne wannan ma’aikata ta fito da shirin tantance sunayen domin su riƙa cin moriyar ayyukan wannan ma’aikata kai-tsaye,” inji ta.

 

Daga nan ta gode wa Gwamnatin Jihar Katsina dangane da ƙoƙarin da ta ke kan yi wa waɗanda hare-haren ‘yan bingida ya shafa.

 

Wasu da hare-haren ‘yan bindiga ya shafa daga ƙananan hukumomin Jibia, Batsari da Kurfi, sun shaida wa jami’an shirin cewa su na buƙatar muhalli.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Daure Dan Acaba Shekara 20 Kan Yi Wa Karamar Yarinya Fyade

Next Post

Akwai Raini Da Nuna Bambanci A Masana’antar Kannywood —Maman Haidar

Related

Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wani Ɗan Bindiga, Sun Ƙwato Makamai Bayan Artabu A Taraba

8 hours ago
Wata Hajiya ‘Yar Nijeriya Mai Shekaru 75 Ta Rasu A Saudiyya Yayin Aikin Hajji
Labarai

Wata Hajiya ‘Yar Nijeriya Mai Shekaru 75 Ta Rasu A Saudiyya Yayin Aikin Hajji

9 hours ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Kisan Wata Matar Aure, ‘Yar shekara 22 A Kano

11 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama A Wani Sabon Hari Da Suka Kai Sansanin Sojoji A Borno
Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama A Wani Sabon Hari Da Suka Kai Sansanin Sojoji A Borno

12 hours ago
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Amso Bashin $21.5bn Da ₦757.9bn

14 hours ago
Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a
Ra'ayi Riga

Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a

15 hours ago
Next Post
Akwai Raini Da Nuna Bambanci A Masana’antar Kannywood —Maman Haidar

Akwai Raini Da Nuna Bambanci A Masana’antar Kannywood —Maman Haidar

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC Karo Na Farko

An Gudanar Da Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC Karo Na Farko

May 27, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wani Ɗan Bindiga, Sun Ƙwato Makamai Bayan Artabu A Taraba

May 27, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashen Afirka

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashen Afirka

May 27, 2025
Sin Za Ta Kara Zurfafa Dunkule Rawar Yankunan Raya Tattalin Arziki Da Fasahohi A Fannin Janyo Jarin Waje

Sin Za Ta Kara Zurfafa Dunkule Rawar Yankunan Raya Tattalin Arziki Da Fasahohi A Fannin Janyo Jarin Waje

May 27, 2025
Yamal Ya Saka Hannu A Sabon Kwantiragin Shekaru 6 A Barcelona 

Yamal Ya Saka Hannu A Sabon Kwantiragin Shekaru 6 A Barcelona 

May 27, 2025
Muhammad Salah: Gwarzon Afirka A Firimiyar Ingila

Ina Fatan Cigaba Da Taka Leda Har Zuwa Lokacin da Zan Cika Shekara 40 A Duniya – Salah

May 27, 2025
Wata Hajiya ‘Yar Nijeriya Mai Shekaru 75 Ta Rasu A Saudiyya Yayin Aikin Hajji

Wata Hajiya ‘Yar Nijeriya Mai Shekaru 75 Ta Rasu A Saudiyya Yayin Aikin Hajji

May 27, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Nuna Misali Na Bude Kofa Da Raya Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da ASEAN Da GCC

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Nuna Misali Na Bude Kofa Da Raya Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da ASEAN Da GCC

May 27, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Kisan Wata Matar Aure, ‘Yar shekara 22 A Kano

May 27, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Kasa Na Yara Jagorori Na Kasar Sin 

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Kasa Na Yara Jagorori Na Kasar Sin 

May 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.