• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hatsarin Mota Ya Hallaka Mutum 5 Da Raunata 2 A Jihar Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

A kalla mutane biyar ne suka rasa rayukansu a wani hatsarin mota da ya auku a kauyen Isma da ke kan babban hanyar Bauchi zuwa Jos a ranar Asabar, kana hatsarin ya jikkata mutum biyu.

Kwamandan shiyya na hukumar kiyaye aukuwar hadura (FRSC) a jihar Bauchi, Malam Yusuf Abdullahi shi ne ya tabbatar da hakan wa ‘yan jarida a jiya, yana mai cewa hatsarin ya auku ne da misalin karfe 7:50 na safiya kuma ya rutsa da mutane bakwai, manyan maza uku, manyan mata uku gami da wata karamar yarinya.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Sace Wani A Bauchi

Yusuf ya ce: “An samu aukuwar wani mummunar hatsari a kauyen Isma da ke kan hanyar Bauchi zuwa Jos a yau (Asabar), 5 ga watan Nuwamban 2023 wajajen karfe 7.50am.”

Ya kara da cewa hatsarin ya faru ne a tsakanin wata motar gida Peugeot 406 mai lamba: KRD649CA da kuma wata babbar motar tankar dakon Mai mallakin kamfanin Mai ta AIB mai lamba: MSA394SA.

A fadinsa, hatsarin ya faru ne sakamakon kauce wa ka’idojin tuki da tsula gudun wuce kima, kana motocin da kadarorin da aka kwaso a wajen da hatsarin ya faru an mika su ga sashin kula da cinkoson ababen hawa ta caji ofis din hukumar ‘yan sanda da ke GRA a Bauchi.

LABARAI MASU NASABA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Ya daura da cewa, “Cikin gaggawa bayan da hatsarin ya wakana, jami’anmu sun garzaya inda abun ya faru cikin mintina 26 da sanar mana, sun kwashi wadanda suka jikkata zuwa asibitin koyarwa ta jami’ar ATBU domin nema musu kulawar likitoci.

“A nan ne likita ya tabbatar da mutuwar mutum biyar a cikinsu, maza biyu, mata biyu da wata yarinya.

“Sauran na miji da macen (Dukka manya) sun gamu da raunuka daban-daban kuma suna amsar kulawar likitoci, an kuma ajiye gawarwakin da suka mutu a dakib adana gawarwai amma daga baya za a mika su ga ahlinsu domin yi musu jana’iza,” ya shaida.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna
Labarai

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga
Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra
Labarai

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Next Post
Shugabannin Duniya Sun Bayyana Baje Kolin CIIE A Matsayin Muhimmin Dandali Na Cin Gajiyar Damammaki

Shugabannin Duniya Sun Bayyana Baje Kolin CIIE A Matsayin Muhimmin Dandali Na Cin Gajiyar Damammaki

LABARAI MASU NASABA

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.