• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hatsarin Mota Ya Hallaka Mutum 5 Da Raunata 2 A Jihar Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Mutum 3 Sun Rasu, 15 Sun Jikkata A Wani Hadarin Mota A Hanyar Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kalla mutane biyar ne suka rasa rayukansu a wani hatsarin mota da ya auku a kauyen Isma da ke kan babban hanyar Bauchi zuwa Jos a ranar Asabar, kana hatsarin ya jikkata mutum biyu.

Kwamandan shiyya na hukumar kiyaye aukuwar hadura (FRSC) a jihar Bauchi, Malam Yusuf Abdullahi shi ne ya tabbatar da hakan wa ‘yan jarida a jiya, yana mai cewa hatsarin ya auku ne da misalin karfe 7:50 na safiya kuma ya rutsa da mutane bakwai, manyan maza uku, manyan mata uku gami da wata karamar yarinya.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Sace Wani A Bauchi

Yusuf ya ce: “An samu aukuwar wani mummunar hatsari a kauyen Isma da ke kan hanyar Bauchi zuwa Jos a yau (Asabar), 5 ga watan Nuwamban 2023 wajajen karfe 7.50am.”

Ya kara da cewa hatsarin ya faru ne a tsakanin wata motar gida Peugeot 406 mai lamba: KRD649CA da kuma wata babbar motar tankar dakon Mai mallakin kamfanin Mai ta AIB mai lamba: MSA394SA.

A fadinsa, hatsarin ya faru ne sakamakon kauce wa ka’idojin tuki da tsula gudun wuce kima, kana motocin da kadarorin da aka kwaso a wajen da hatsarin ya faru an mika su ga sashin kula da cinkoson ababen hawa ta caji ofis din hukumar ‘yan sanda da ke GRA a Bauchi.

Labarai Masu Nasaba

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Ya daura da cewa, “Cikin gaggawa bayan da hatsarin ya wakana, jami’anmu sun garzaya inda abun ya faru cikin mintina 26 da sanar mana, sun kwashi wadanda suka jikkata zuwa asibitin koyarwa ta jami’ar ATBU domin nema musu kulawar likitoci.

“A nan ne likita ya tabbatar da mutuwar mutum biyar a cikinsu, maza biyu, mata biyu da wata yarinya.

“Sauran na miji da macen (Dukka manya) sun gamu da raunuka daban-daban kuma suna amsar kulawar likitoci, an kuma ajiye gawarwakin da suka mutu a dakib adana gawarwai amma daga baya za a mika su ga ahlinsu domin yi musu jana’iza,” ya shaida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Ya’yan Jam’iyyar PDP Sama Da 1,000 Sun Sauya Shekar Siyasa Zuwa APC A Zamfara

Next Post

Shugabannin Duniya Sun Bayyana Baje Kolin CIIE A Matsayin Muhimmin Dandali Na Cin Gajiyar Damammaki

Related

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

6 hours ago
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci
Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

8 hours ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

9 hours ago
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

10 hours ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

11 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

12 hours ago
Next Post
Shugabannin Duniya Sun Bayyana Baje Kolin CIIE A Matsayin Muhimmin Dandali Na Cin Gajiyar Damammaki

Shugabannin Duniya Sun Bayyana Baje Kolin CIIE A Matsayin Muhimmin Dandali Na Cin Gajiyar Damammaki

LABARAI MASU NASABA

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

May 9, 2025
Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

May 9, 2025
Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

May 9, 2025
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

May 9, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.