• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hidimta Wa Al’umma Shi Ne Babban Burina -Injiniya Hassan

by Bello Hamza
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Hidimta Wa Al’umma Shi Ne Babban Burina -Injiniya Hassan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Injiniya Hassan Mohammed shi ne Sarkin Yakin Garkuwan Keffi Janar TY Buratai kuma shugaban kungiyar kwallon kafa na TY Buratai Football Academy da ke garin Keffi ta Jihar Nasarawa.

Yana daya daga cikin matasan yankin Arewacin Nijeriya masu hangen nesa a halin yanzu, wadanda Allah ya azurta da halaye irin na dattawa.

  • Hukumar Harkokin Waje Ta NPC Ta Fitar Da Sanarwa Kan Kudurin Amurka Game Da Shigar Balan Balan Din Sin Samaniyar Amurka
  • An Saurari Bayani Game Da Yanayin Yaki Da Cutar COVID-19 Na Kasar Sin

Injiniya Hassan ya sadaukar da rayuwarsa wajen ganin matasa sun kaurace wa duk wani abin da zai cutar da rayuwarsu sun kuma rungumi sana’o’in dogaro da kai; a kan haka ya yi ruwa ya yi tsaki wajen ganin nasarar kungiyar kwallon kafa wadda aka sadaukar da ita ga tsohon shugaban rundunar sojojin Nijeriya Janar TY Buratai, kungiyar ta zama kafar samar wa matasa  abin yi wanda da dama daga cikinsu sun samu rufin asiri a harkar kwallon kafa.

Mataimakin Editanmu Bello Hamza ya tafi takanas ta Kano zuwa garin Keffi ta Jihar Nasarawa inda ya tattauna da shi, ya yi bayanai da dama a kan abin da ya shafi rayuwarsa, harkokinsa na tallafa wa al’umma da kuma yadda ya karbi karramawar da kungiyar ‘Arewarmu Duniyarmu’ ta yi masa a ranar 11 ga watan Fabrairu 2023 da mukamin Matawallen Arewa (Jakadan Zaman Lafiya) a bikin da aka yi a fadar Sarkin Bauchi da ke Jihar Bauchi, ga dai yadda hirar tasu ta kasance:

Da Farko Zamu So Mu Ji Takaittacen Tarihinka

Labarai Masu Nasaba

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

Suna na Injiniya Hassan Mohammed an haife ni ne a shekarar 1980 a karamar hukumar Yusufari ta Jihar Yobe, na yi makarantar frimare a tsakanin garin Yusufari ta Jihar Yobe da kasar Jumhoriyyar Nijar, daga baya na dawo gida Nijeriya inda na cigaba da karatu a Federal Polytechnic Damaturu ta Jihar Yobe inda na yi ‘National Diploma’ a ‘Cibil Engineering’ sannan na kuma yi ‘Higher National Diploma’ a ‘Federal Polytechnic’ Bauchi daga baya na shiga Jami’ar Tafawa Balewa ATBU don samun babbar difloma ‘Post-graduate Diploma’ duk a bangaren ‘Cibil Engineering Technology, na kuma yi kwasa-kwasai masu yawa a bangarorin ilimi da dama.

Ta Yaya Ka Samu Kanka A  Gaba Wajen Harkokin Tallafa Wa Al’umma?

Wato tun asali na taso ne a cikin iyali da al’umma da suka dauki harkokin tallafa wa al’umma da mutukkar muhimmanci, a haka na taso na ci gaba da koyi da haka, na samu karfafawar shugaba na kuma abin koyi na Tsohon Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya, Janar TY Buratai CFR Garkuwan Keffi, wanda ya yi matukar tasiri a rayuwa na, nima a kan haka na ci gaba da koyi da wannan hali nasa, ni kuma ina yin daidai gwargwardon abin da zan iya yi na ganin matasa sun samu kyakyawan rayuwa.

Wacce Gudummawa Kungiyar Kwallon TY Buratai Football Academy Ke Badawa Wajen Bunkasa Rayuwar Matasa?

Harkar kwallo na taka gaggaruwar rawa wajen bunkasa rayuwar matasa a sassan duniya kuma ana samun kudade masu yawa a harkar wasan kwallo a duniya, a kan haka muma a kungiyar kwallo ta TY Buratai Football Academy da aka kafa a shekarar 2021, muna fatan bayar da tamu gudumwar daidai gwargwadon yadda zamu iya. Tun da aka kafa kungiyar a shekarar mun samu nasararori da dama a wassanin da muka yi a ciki da wajen kasar nan, yan wasanmu kuma suna nuna bajintar da ya kamata a dukkan wasan da suka buga. Wannan nasarorin suna kuma samuwa ne saboda cikakkiyar goyon bayan da muke samu daga shugabanmu wato Janar TY Buratai wanna Allah ya sanya masa soyayyar ci gaban matasa, yana kuma bamu dukkan goyon bayan da muke bukata. Muna fatan wata rana zamu samu kanmu a cikin rukunin manyan kungiyoyin kwallo na kasar nan, inda zamu fitar da kasarmu kunya a matakai daban-daban.

Ya Ka Samu Kanka Da Mukamin Sarkin Yakin Garkuwan Keffi?

Kamar dai yadda ka gani, ni ina matsayin Sarkin Yakin Garkuwan Keffi ne wato, Janar T Y Buratai, shi ne aka nada a mastayin Garkuwan keffi, masarautar Keffi ta yi haka ne saboda irin gudummawarsa ga al’umma Keffi, musamman irin gaggrumar ci gaba da ya samar a masarautar Keffi da kewaye dama Jihar Nasarawa gaba daya. Bayan nada shi ne ya yi min wannan nadin na Sarkin Yakin a fadarsa, ina matukar alfahari da sarautar don duk inda aka ambaci suna na sai an hada da Sarkin Yakin Garkuwan Keffi ina kuma mutukar alfahari da hakan. A kan haka ina addu’ar Allah ya kara wa Garkuwan Keffi lafiya da tsawon kwana, Allah kuma ya albarkaci masarautar Keffi, Jihar Nasarawa da Nijeriya baki daya.

Ya Kuma Ka Karbi Sarautar Matawallen Arewa (Jakadan Zaman Lafiya) Da Kungiyar ‘Arewarmu Duniyarmu’ Ta Yi Maka?

Tabbas wannan nadin na kungiyar ‘Arerwarmu Duniyarmu’ ta zo mani a matsayin bazata, ban taba sa rai ba, sai kawai naga wasika daga kungiyar wadda shugabanta Alhaji Haruna Ibrahim da kuma sakataren kungiyar Kwamrade Isah Sulaiman suka sanya wa hannu inda suke bayanin dalilai da yadda suka cimma shawarar karramani da wannan sarauta ta Matawallen Arewa jakadan zaman lafiya wani taron su na shekara-shekara da suka yi a fadar mai martaba Sarkin Bauchi. Na yi farin cikin samun wannan yabon, musamman na fahinci cewa, dan abin da nake yi har wasu sun bi diddigi za su karrama ni a kai, hakan ya kara mani karfin gwiwa da zimmar ganin na kara kaimi wajen hidimta wa al’umma. Abin ya fi bani sha’awa a shirin taron da za a yi shi ne yadda suka tattaro mahayan dokuna daga sassan Arewacin Nijeriya inda suka baje koli tare da gabatar da wata kwarkwayar Daba wanda da mahaya fiye 150 suka halarta, ga kuma makida da mawakanmu na gargajiya suma sun baje fasahar da Allah ya basu. Addu’a na a nan shi ne Allah ya saka musu da alhairi.

Wacce Shawara Kake Da Shi Ga Matasa Musaamman A Wannan Lokacin Da Ake Fuskantar Zabe?

Yakamata matasa su fahinci cewa sune kashin bayan al’umma saboda haka bai kamata su bari wasu ‘yan siyasa da ‘yan barandan su lalata musu rayuwa ba, bangar siyasa ba alhairi ba ne, al’amari ne da ke jefa rayuwar masu yi cikin hatsari, in har bangar siyasa abin yi ne mai zai sa ‘yan siyasar ba za su kawo yaransu ba, suna can suna karatu a kasashen waje amma suna ba yaran wasu kwayoyi don su biya musu bukata. Ina mai kira a gare su da su yi karatun ta natsau, su rungumi zaman lafiya tare da sana’o’in dogaro da kai.

Menene Zaka Ce Ga ‘Yan Siyasan Kuma?

Ina kiga gare su da su ji tsoron Allah su sani cewa Allah yana kallon abin da suke yi kuma zai tambaye su ayyuykan da suka yi saboda haka su guji sanya yaran talakawa hanyar halaka. Ina amfani da wannan damar na addu’ar Allah ya zaba mana shugabanni na gari masu tausayin talakawa, Allah kuma ya sa a yi zaben lafiya ba tare da wata mastaala ba.

Me Zaka Ce Ga Wadanda Suka Samu Halartar Taron?

Ina mika godiya ta musamman ga Ambasada Tukur Yusufu Buratai CFR tsohon shugaban rundunar sojojin Nijeriya kuma Garkuwan Keffi, ina addu’ar Allah ya kare mana shi ya kuma kara masa daukaka duniya da lahira. Ina kuma godiya ga dukkan wadanda suka samu halartar taron kamar su Sadaukin Garkuwan Keffi Hon. Ibrahim Danfulani da Bulama Ibrahim Buratai, Sultan Alhassan, Col. Haruna Idris Zaria, Ibrahim Sani Garba, da kuma Injiniya Usman Ahmed Injiniya Hassan Geidam, Injjiniya Adamu Bahago Dagona, Zanna Dapchi, shugaban karamar hukumar Bursari ta Jihar Yobe, da dan majalisa wakilai, Hon. Kabir Lawal Jarman Garkuwan Keffi, Injiniya Mohammed Abbagana, Injiniya Hassan Bilal, Surb. Ali Badema, Surb. Hassan Gambo, Ali Alhaji Audu P.A, Musa Jajere, Injiniya Adamu Idi, Engr Idriss Yerima, Injiniya Adamu Ibrahim, Injiniya Mohd Ibn Adam, Mohammed Hassan Jajere, na gode kwarai da gaske.

To Ranka Ya Dade Mun gode

Nima na gode


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: InjiniyaJihar NasarawaKwallon Kafa
ShareTweetSendShare
Previous Post

DSS Ta Bankado Shirin Boko Haram Na Kai Wa Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Hari

Next Post

NIS Ta Yi Wa Jami’ai Sama 60 Karin Girma

Related

Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

10 hours ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

15 hours ago
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja
Manyan Labarai

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

16 hours ago
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa
Manyan Labarai

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

18 hours ago
Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa
Manyan Labarai

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

18 hours ago
Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

1 day ago
Next Post
NIS Ta Yi Wa Jami’ai Sama 60 Karin Girma

NIS Ta Yi Wa Jami'ai Sama 60 Karin Girma

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.