• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hisbah Ta Haramtawa Maza Masu Kiɗan DJ Shiga Wurin Shagalin Bikin Mata A Jihar Kano

by Naziru Adam Ibrahim
1 year ago
in Labarai
0
Hisbah Ta Haramtawa Maza Masu Kiɗan DJ Shiga Wurin Shagalin Bikin Mata A Jihar Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta haramtawa maza masu yin DJ (kaɗe-kaɗe) gudanar da kaɗe-kaɗe a yayin taron bukukuwan da mata suka mamaye, a duk fadin jihar.

Babban kwamandan hukumar, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ne ya bayyana hakan a lokacin da yake ganawa da wakilan masu kaɗe-kaɗen a jihar.

  • Hajjin 2024: Ranar 10 Ga Watan Yuni Za A Kammala Jigilar Maniyyata – NAHCON
  • Jami’ar FUBK Ta Gudanar Da Bikin Ɗaukar Sabbin Ɗalibai 2, 217 A Kebbi

Sheikh Daurawa ya jaddada cewa, haramcin na da nufin hana cakuduwar maza da mata a lokutan bukukuwan al’umma, inda ya yi nuni da cewa, cakuduwa tsakanin maza da mata ya sabawa al’adar jihar da addinin Musulunci.

Ya jaddada cewa, kasancewar dokokin Musulunci jihar ke dogaro da shi, ya zama wajibi a kiyaye ka’idojin da ke hana ayyukan da ake ganin sun saba wa koyarwar Musulunci.

Sheikh Daurawa ya bayyana cewa, daga yanzu mata ne kawai za a bari su gudanar da taron mata.

Labarai Masu Nasaba

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

Bugu da kari, Sheikh Daurawa ya bayyana cewa, kafin yanke wannan hukunci, hukumar ta Hisbah ta hada hannu da masu cibiyoyin taro da manajojinsu a jihar domin wayar musu da kai kan dokokin da ke tafiyar da harkokinsu.

A nasa martanin, wakilin makaɗan, DJ Ibrahim Abdullahi wanda aka fi sani da DJ Farawa, ya nuna godiya ga hukumar ta Hisbah bisa gayyata da jagoranci da aka yi musu.

Ya bayyana muhimmancin bin sabbin ka’idojin da hukumar ta bullo da su, musamman dangane da tsarkin lokutan sallah da kuma ware tsakanin maza da mata a lokutan bukukuwan jama’a.

Abdullahi ya bukaci dukkan makaɗan da ke aiki a fadin jihar da su yi rajista da kungiyarsu domin tabbatar da bin ka’idojin hukumar ta Hisbah wanda yace, kungiyar ba za ta kare duk wani DJ da aka samu da laifi ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Al'adun kasar HausaDJ FarawaHisbahShari'ar Musulunci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Inuwa Ya Ƙaddamar Da Sabon Kamfanin Taki A Gombe

Next Post

JAMB Ta Sake Fitar Da Wasu Sakamakon Jarrabawa 36,540

Related

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

2 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

4 hours ago
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
Labarai

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

5 hours ago
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

7 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

8 hours ago
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
Labarai

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

9 hours ago
Next Post
JAMB Ta Sake Fitar Da Wasu Sakamakon Jarrabawa 36,540

JAMB Ta Sake Fitar Da Wasu Sakamakon Jarrabawa 36,540

LABARAI MASU NASABA

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

September 17, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.