• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Haraji Ta Nemi A Samar Da Dokar Sa Ido A Kan ‘Yan Kirifto

by Bello Hamza and Sulaiman
12 months ago
in Tattalin Arziki
0
Hukumar Haraji Ta Nemi A Samar Da Dokar Sa Ido A Kan ‘Yan Kirifto
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Hukumar Tattara Haraji ta Kasa, Zacch Adedeji ya bayyana cewa, a halin yanzu hukumar ta kammala shirin tunkarar Majalisar Kasa don a samar da dokar da za ta sa ido a kan harkokin ‘yan Kirifto a Nijeriya.

 

Adedeji ya bayyana haka ne a taron masu ruwa da tsaki tare da’yan kwamitin majalisar dattawa da na wakilai a kan harkokin kudi da aka yi a Legas a makon jiya.

  • Kisan Gillar Basaraken Daular Gobir A Hannun Masu Garkuwa Ta Girgiza Al’umma
  • Kasar Sin Ta Harba Sabon Tauraron Dan Adam Na Sadarwa

Ya ce, matakin farko shi ne an samar da dokar da za ta sanya ido a kan harkokinsu, shi ya sa kuka ga ‘yan majalisar kasa gaba daya a wannan taron, wannan ne matakin farko, haka kuma ake yi a ko’ina a duniya, in aka samu bullar wani sabon lamari kamar wannan, saboda haka dole ka shirya fuskanta lamarin domin ba za a iya kauce masa ba. Muna shirin sanya ido a kai ta yadda ba zai yi illa ga tattalin arzikin Nijeriya ba.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

Sabon Shugaban Matatar Dangote Ya Bayyana Shirin Faɗaɗa Ayyukanta

Ya kuma ce, hukumar ta yi hankoron samar da harajin fiye da na Naira Tiriliyan 19.4 daga bangarori daban daban a shekarar 2024.

 

A kan wasu haraji kuma kamar ‘stamp duty’, ya ce, “Wasu dokokin haraji da kasar nan ke amfani da su an kafa su ne tun shekarar 1939. A lokacin kuma ba mu da gwamnmatin jihohi da na kananan hukumomi, saboda haka ne shugaban kasa ya kafa kwamitin domin sake nazarin dokokin kasa tare da samar da mafita domin ciyar da kasa gaba.”

 

Adedeji ya kuma ce, “Zuwa watan Satumba za a gabatar wa da majalisar kasa sabbin doka wanda zai zama matakin farko na daidaita harkokin masu sana’ar Kiripto a Nijeriya.”

 

“A yau ba za mu iya kauce wa daga harkokin ‘yan kirifto ba, amma kuma abin mamaki shi ne babu wata doka a fadin kasar nan da ta sanya ido a harkokin ‘yan kirifto. Kuma ba za mu iya kawar da ido daga harkokinsu ba.”

 

A nasa tsokacin, shugaban kwamitin majaliar dattawa a kan harkokin kudi, Sanata Muhammed Musa ya ce, majalisar kasa za ta yi aiki tare da dukkan masu ruwa da tsaki domin karfafa hjanyoyin karbar haraji a fadin kasar nan.

 

“A kan haka aka samu hadin kai tsakanin majalisar dattawa da majalisar wakilai don cimma wannan manufar” in ji shi


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin: Taron Koli Na FOCAC Zai Ba Da Damar Tattauna Shirin Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Next Post

Xi Jinping Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Firaministan Birtaniya

Related

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji
Tattalin Arziki

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

3 days ago
Sabon Shugaban Matatar Dangote Ya Bayyana Shirin Faɗaɗa Ayyukanta
Tattalin Arziki

Sabon Shugaban Matatar Dangote Ya Bayyana Shirin Faɗaɗa Ayyukanta

4 days ago
Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa
Tattalin Arziki

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

4 days ago
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA
Tattalin Arziki

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

2 weeks ago
Dangote
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

3 weeks ago
Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote
Tattalin Arziki

Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote

3 weeks ago
Next Post
Xi Jinping Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Firaministan Birtaniya

Xi Jinping Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Firaministan Birtaniya

LABARAI MASU NASABA

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

August 5, 2025
Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

August 5, 2025
Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

August 5, 2025
Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

August 5, 2025
Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

August 5, 2025
Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar

Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar

August 5, 2025
Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina

Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina

August 5, 2025
Sashen Cinikayyar Samar Da Hidimomi Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso Takwas A Rabin Farko Na Shekarar 2025

Sashen Cinikayyar Samar Da Hidimomi Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso Takwas A Rabin Farko Na Shekarar 2025

August 5, 2025
Gwamnatin Sin: Gwamnatin Jama’a Domin Jama’a

Gwamnatin Sin: Gwamnatin Jama’a Domin Jama’a

August 5, 2025
Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa

Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa

August 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.