• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Haraji Ta Nemi A Samar Da Dokar Sa Ido A Kan ‘Yan Kirifto

byBello Hamza and Sulaiman
1 year ago
Haraji

Shugaban Hukumar Tattara Haraji ta Kasa, Zacch Adedeji ya bayyana cewa, a halin yanzu hukumar ta kammala shirin tunkarar Majalisar Kasa don a samar da dokar da za ta sa ido a kan harkokin ‘yan Kirifto a Nijeriya.

 

Adedeji ya bayyana haka ne a taron masu ruwa da tsaki tare da’yan kwamitin majalisar dattawa da na wakilai a kan harkokin kudi da aka yi a Legas a makon jiya.

  • Kisan Gillar Basaraken Daular Gobir A Hannun Masu Garkuwa Ta Girgiza Al’umma
  • Kasar Sin Ta Harba Sabon Tauraron Dan Adam Na Sadarwa

Ya ce, matakin farko shi ne an samar da dokar da za ta sanya ido a kan harkokinsu, shi ya sa kuka ga ‘yan majalisar kasa gaba daya a wannan taron, wannan ne matakin farko, haka kuma ake yi a ko’ina a duniya, in aka samu bullar wani sabon lamari kamar wannan, saboda haka dole ka shirya fuskanta lamarin domin ba za a iya kauce masa ba. Muna shirin sanya ido a kai ta yadda ba zai yi illa ga tattalin arzikin Nijeriya ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho

Ya kuma ce, hukumar ta yi hankoron samar da harajin fiye da na Naira Tiriliyan 19.4 daga bangarori daban daban a shekarar 2024.

 

A kan wasu haraji kuma kamar ‘stamp duty’, ya ce, “Wasu dokokin haraji da kasar nan ke amfani da su an kafa su ne tun shekarar 1939. A lokacin kuma ba mu da gwamnmatin jihohi da na kananan hukumomi, saboda haka ne shugaban kasa ya kafa kwamitin domin sake nazarin dokokin kasa tare da samar da mafita domin ciyar da kasa gaba.”

 

Adedeji ya kuma ce, “Zuwa watan Satumba za a gabatar wa da majalisar kasa sabbin doka wanda zai zama matakin farko na daidaita harkokin masu sana’ar Kiripto a Nijeriya.”

 

“A yau ba za mu iya kauce wa daga harkokin ‘yan kirifto ba, amma kuma abin mamaki shi ne babu wata doka a fadin kasar nan da ta sanya ido a harkokin ‘yan kirifto. Kuma ba za mu iya kawar da ido daga harkokinsu ba.”

 

A nasa tsokacin, shugaban kwamitin majaliar dattawa a kan harkokin kudi, Sanata Muhammed Musa ya ce, majalisar kasa za ta yi aiki tare da dukkan masu ruwa da tsaki domin karfafa hjanyoyin karbar haraji a fadin kasar nan.

 

“A kan haka aka samu hadin kai tsakanin majalisar dattawa da majalisar wakilai don cimma wannan manufar” in ji shi

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama
Tattalin Arziki

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

October 3, 2025
Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho
Tattalin Arziki

Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho

October 3, 2025
Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG
Tattalin Arziki

Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

September 27, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Firaministan Birtaniya

Xi Jinping Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Firaministan Birtaniya

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version