ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kisan Gillar Basaraken Daular Gobir A Hannun Masu Garkuwa Ta Girgiza Al’umma

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto, Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
2 years ago
Gobir

Kisan gillar babban basarake Daular Gobir, Sarkin Kudun Gatawa, Alhaji Muhammad Bawa a hannun ‘yan bindiga, ta yi matukar girgiza al’ummar jihar Sakkwato wadanda rasuwarsa a hannun ‘yan bindigar ta zo masu a- ba- zata a yayin da suke tsammamin dawowarsa a cikin iyali lafiya.

 

A yayin da al’ummar Sakkwato suke jimami da jajantawa kan faruwar mummunan al’amarin tare da dora alhakin hakan ga gwamnati haka ma bayanai daga masarautar Gobir da Gabashin Sakkwato ya nuna al’amurra sun tsaya cik!

ADVERTISEMENT
  • Yadda Ambaliya Ta Lalata Gidaje 255 A Garin Natsinta Da Ke Katsina
  • Gwamnatin Kano Za Ta Tsara Zamantar Da Magungunan Gargajiya

Al’umma sun shiga cikin kunci da takaicin yadda basaraken wanda aka shaida da gudanar da mulkin gaskiya da adalci ya rasa ransa a hannun ‘yan bindigar duk kuwa da ikirarin da Gwamna Ahmed Aliyu ya yi a yayin yekuwar neman zabe cewa, idan duka kudin jihar Sakkwato za su kare sai gwamnatinsa ta samar da ingantaccen tsaro a Gabashin Sakkwato.

 

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

A cikin bidiyon da aka saki a karshen mako, an ga basaraken cikin yanayi na tashin hankali, sanye da tufafin da suka jike da jini kuma daure da sarkoki, yana rokon gwamnatin da ya ce ya hidimta mata tsawon shekara 45 ta taimaka masa a wannan mawuyacin hali.

 

Dangane da lamarin, wani dan Majalisar Dokoki ta Jihar Sakkwato, Honarabul Aminu Boza, ya tabbatar da cewa mutumin da ke cikin bidiyon shi ne basaraken da aka sace.
Iyalin Sarkin sun nuna damuwa da takaici kan yadda suka sanar da hukuma, amma ba a sami cikakkiyar kulawa ba. Sun bayyana cewa duk da kokarin tattaunawa da masu garkuwar da suka yi, wadanda suka sace shi sun nace sai gwamnati ta shiga lamarin kafin a sako shi.

 

A hirarsa da BBC, Shuaibu Gwanda Gobir, wanda shi ne magajin garin na Gobir kuma daya daga cikin masu nadin sarki, ya ce labari ya ishe su cewa masu garkuwar sun kashe sarkin ne a ranar Talata.

 

“Labarin da na samu shi ne ‘yan bindigar sun harbe shi ne tun a jiya Talata bayan la’asar, kuma wadanda suka je tattauna biyan kudin fansa ne suka ga gawar sarkin a kwance,” in ji shi.

 

Ya kara da cewa zuwa lokacin da aka yi magana da shi ba su karbi gawar mai martaban ba tukunna.

 

Kazalika, ya ce akwai dan sarkin mai suna Kabiru da aka yi garkuwa da su tare, kuma abin da suka saka a gaba kenan yanzu.
Magajin garin ya ce: “A ranar Talata da safe an kira shugaban masu garkuwar har ma yana tambaya game da kudin fansa. Da aka nemi a yi magana da sarkin sai ya ce yana can yana jin dumi a gefen wuta.

 

“Da aka yi magana da Kabiru ya tabbatar da cewa sarki na can yana jin dumi, amma ya yi ta rokon a biya kudin fansa domin kubutar da su.”

 

Wani dan sarkin na Gobir ya ce an yi wa mahaifin nasa kwanton-bauna ne a yankin Kwanar Maharba yayin da yake komawa gida.

 

“‘Yan bindigar sun fara harbi kan mai uwa da wabi lokacin da suka hangi motar mahaifin namu, abin da kuma ya janyo fashewar tayoyin motar da karkatar da hankalin direbansa har ta kai ya tsaya,” in ji dan sarkin.

 

Majiyoyi daga Sabon Birni sun ce an yi garkuwa da karin mutum biyar a yankin a ranar da aka sace sarkin.

Gobir
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ posts Bio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    A Yayin Da Babban Bankin Ƙasa (CBN) Ke Yaƙi Da Laifukan Intanet
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Halin Da Matsalar Tsaro Ta Jefa ‘Yan Gudun Hijira A Arerwacin Nijeriya
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Sanata Tambuwal Ya Sadaukar Da Takararsa Ga Faruku Yabo
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Dan-Iya Ya Zama Ɗan Takarar Gwamnan ADC A Sakkwato
Gobir
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya
Gobir
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
ASUU

Dalilai 5 Da Suka Sa ASUU Barazanar Sake Tsunduma Yajin Aiki

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.