• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

by Bello Hamza and Sulaiman
6 months ago
NPA

Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA, ta bayar da tabbacin cewa, aikin samar da sauki a hada-hadar jigilar kaya na kasa wato NSWP, za a kammala shi a zango na daya a 2026.

 

Wannan na zuwa ne, bayan da Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya amince da a zamanantar da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Apapa da ta Tin Can Island.

  • Har Yanzu Manyan ‘Yan Wasa Suna Son Buga Wasa A Manchester United – Amorim
  • Masana Sun Bayyana Yadda Yakin Neman Zaben 2027 Ke Barazana Ga Harkokin Tafiyar Da Gwamnati

Shugabanta Dakta Abubakar Dantsoho ya sanar da haka a yayin da yake yiwa baki jawabi a yayin kadammar da kwamtin tabbatar da ingnaci da za su sa ido kan ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa da kuma na Hukumar Kwastam ta Kasa, wato PCEC da aka gudanar a ranar Alhamis a jihar Legas.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025, Kamfanin Nestlé Pure Life

Cibiyar samar da kyakyawan yanayin yin kasuwanci na Fadar Shugaban Kasa da hadaka da NPA ne, suka shirya taron kaddamarwar,

 

“Ana sa ran a zangon farko na 2026, aikin na NSWP zai fara fara aiki wanda tuni, Fadar Shugaban Kasa ta amince da kwangilar domin a wanzar da aikin,” Inji Dantsoho.

 

Ya kuma bayar da tabbacin cewa, za a rinka gudanar da ganawa akai-akai da masu ruwa da tsaki domin gudanar da hada-hadar kasuwanci a cikin Tashoshin Jiragen Ruwan kasar a cikin nasara.

 

Ya sanar da cewa, zuba hannun jari a kayan aiki Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar, samar da kayan aiki na fasahar zamani da sauransu, za su taimaka wajen kara habaka kasa da kuma gudanar da ayyuka, a Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar.

 

Dantsoho ya kara da cewa, kayan aikin da ke a musamman Tashoshin Jiragen Ruwa na Apapa da Tin Can Island, sun jima ana yin amfani da su a kasar nan, wadanda kuma akwai bukatar a yi masu garanbawul.

 

“Yau kimanin shekaru 48 ke nan, da kafa Tashar Jirgin Ruwa ta Tin Can Island, inda kuma ta Apapa ta kai kimanin shekaru 100, amma har yanzu, ba a yi masu wani garanbawul ba,” A cewar Dantsoho.

 

Sai dai, ya sanar da cewa, amincewar kwanan baya da Gwamnatin Tarayya ta yi na a yiwa daukacin Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar garanbawul, hakan zai kara taimakawa wajen gudanar da ayyuka a Tashoshin.

 

A bangaren kimiyya Shugaban ya bayyana cewa, Hukumar na ci gaba da aiki kafada da kafada da kungiyar kula da harkokin teku ta kasa da kasa wato IMO, domin yin amfani da tsarin PCS, duba da cewa, inda ya alakanta aikin na NSWP, a matsayin wani banban ginshiki.

 

Dantsoho ya jadda cewa, tsarin na PCS, zai kawar da yin amfani da takardu, da kuma yin shisshigi, wanda hakan zai kuma kara tabbatar da kawar da duk wata badakala da za ta iya kunno kai da rage tsada da kuma kara samar da kudaden shiga.

 

“Hukumar ta NPA kadai, ba za ta yi cimma burin da ta sanya a gaba sai ba, sai an hada karfi da karfe kuma kara tabbatar da inganci, abu ne da ya karade kowanne fanni, matukar muna son kara samar da karin kudaden shiga wadanda za su yi daidai da na fadin duniya ,” , A cewar Dantsoho.

 

A na ta jawabin, Darakta Janar ta Kwamitin Gudanar da Muhalli na Kasuwanci na Shugaban kasa (PEBEC) Princess Zahrah Mustapha Audu ta bayyana cewa, inganganta ayyukan, za su taimaka wajen rage cunkson Jiragen Ruwa a Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar.

 

A cewarta, an kaddmar da Kwamitin ne, domin a samar da sauye-sauye rashin damar da ba a samu a fannin ayyukan Tashihin da kuma kara bunkasa tattalin arzikin kasar nan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria
Tattalin Arziki

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

October 25, 2025
Tattalin Arziki

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025, Kamfanin Nestlé Pure Life

October 25, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA
Tattalin Arziki

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Next Post
Bayan Fara Binciken $2.96bn, An Samu N80bn A Asusun Tsohon Daraktan Kamfanin NNPCL

Bayan Fara Binciken $2.96bn, An Samu N80bn A Asusun Tsohon Daraktan Kamfanin NNPCL

LABARAI MASU NASABA

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Ba Za A Samu Ƙarancin Man Fetur A Lokutan Bukukuwan Ƙarshen Shekara Ba – Dangote 

October 27, 2025
An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga 

An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga 

October 27, 2025
NPA

Tsohon Gwamnan Jigawa, Lamido Ya Bayyana Aniyar Takarar Shugabancin Jam’iyyar PDP Na Ƙasa

October 27, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.