Wakilan kasashe 33 sun sa hannu kan yarjejeniyar kafa hukumar shiga tsakani ta duniya, a yankin Hong Kong na kasar Sin a jiya Jumma’a. Bisa tsarin yarjejeniyar, bayan kasashe sama da 3 sun zartar da yarjejeniyar bisa dokokinsu na cikin gida, to, hukumar shiga tsakani za ta kafu a hukumance. Saboda haka ana sa ran ganin farawar aikin hukumar a farkon shekarar 2026, wadda za ta kafa hedkwatarta a yankin Hong Kong.
Abin lura shi ne, yawancin kasashe daga cikin kasashen da suka sanya hannu, kasashe ne da tattalin arzikinsu ke kan hanyar tasowa. Kana sauran wasu kasashe fiye da goma, da suka kasance a nahiyoyin Asiya, da Afirka, da Latin Amurka, da Turai, sun tura wakilai don gane ma idanunsu bikin kulla yarjejeniyar.
- Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
- Amurka Za Ta Girbi Abin Da Ta Shuka A Kan Matakin Soke Takardar Bizar Karatu Ga Dalibai Sinawa
An ce, a baya yayin da ake neman daidaita sabanin ra’ayi a duniya, kusan an kasa kare moriyar kasashe masu tasowa. Sai dai a nan gaba hukumar shiga tsakani za ta samar musu da sabuwar hanyar daidaita sabanin ra’ayi da rikici.
A ganin kasar Sin, kafuwar hukumar za ta ba da damar kara shigar da kasashe masu tasowa cikin aikin kula da al’amuran duniya, da tabbatar da daidaita rikici ta wata hanya mai adalci, da bai wa kasashe masu tasowa karin ikon fadin albarkacin bakinsu.
A shekarun baya, kasar Sin ta taimaka wajen tabbatar da samun sulhu tsakanin kasar Saudiyya da ta Iran, da ganin yadda bangarorin siyasa daban daban na Falasdinawa suka kulla yarjejeniyar sulhu a birnin Beijing na Sin. Kana a wannan karo, kasar Sin ta taka muhimmiyar rawa a kokarin kulla yarjejeniyar kafa hukumar shiga tsakani. Duk wadannan abubuwa sun nuna yadda Sinawa suke darajanta sulhu da zaman lumana a duniya. (Bello Wang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp