• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Huldar Banki Da Babu Ruwa: Bankin TAJ Ya Samu Ribar Naira Biliyan 6 A Zangon Farko

by Bello Hamza
2 years ago
Taj

Bakin TAJBank, bankin da ake a kan gaba a Nijeriya wajen aiki da kimiyya da fasaha da ke gudanar da harkokinsa ba tare da bayar ko karbar ruwa ba ya sake cirar tuta inda ya zama zakara a cikin watanni shida na farkon shekarar 2023.

Haka kuma masu binciken kudaden bankin sun bayar da sanarwa cewa, bankin ya samu gagarumin ribar da ta kai na Naira Biliyan N6.019 wanda wannan ne riba mafi girma da aka samu a bangaren bankuna a cikin wannan lokacin da ake magana.

  • Kungiyar Kasar Sin Ta Lashe Dukkan Lambobin Zinare Na Wasannin Nutso A Gasar Wasannin Kasashen Asiya
  • Me Ya Sa Aka Kasa Shawo Kan Matsalar Hare-haren Bindiga A Kasar Amurka?

Wannan nasarar yana zuwa ne bayan kasa da wata 6 da bankin ya ba masu hannun jarinsa kudade masu kauri a karshen shekarar kudi ta 2022, wannan kuma na zuwa ne kasa da shekara 3 da shigarsu fagen harkokin bankunan kasar nan kuma hakan wani abu ne da babu wata bankin da ta taba samu a tsawon tarihin harkar banki na shekara 100 a Nijeriya.

TAJBank ya kuma kafa tarihi a farkon wannan shekara a matsayin kamfanin hada-hadar kudi na farko da ya bayyana mallaka kaddarar ‘Sukuk Bond’ na Naira Biliyan 100 a bangaren hada-hadar kudaden kasashen wajen Nijreriya.

Haka kuma kididdigar yadda bankin ya gudanar da harkokinsa ya nuna cewa, shi ne a kan gaba wajen fitar da sabbin hanyoyin bayar da bashi mara ruwa inda a zangon farko na shekarar 2023 aka nuna cewa, sun samu riba da kaddamar da kaddarori da suka kai na Naira Biliyan 212.021 a watan Disamba na shekarar 2022 zuwa Naira biliyan 335.017  har zuwa karshen watan Yuni na shekarar 2023, karuwar ya zama daida da kashi 58 ta kuma samu karin kudin shiga da ya kai kashi 67 daga abin da ta samu na naira biliyan 136.149 a karshe watan Disamba 2022 zuwa naira Biliyan 227.031 a karshen watan Yuni na wannan shekarar.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida

Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho

Wasu nasarorin da bankin ya samu a zangon farko na shekarar 2023 sun hada da yadda hada-hadar bankin ya karu da kashi 62 daga naira biliyan 78.235 da aka samu a watan Disamba 2022 zuwa Naira Biliyan 126.725 a zangon farko na shekarar 2022; yayin da kaddarar bankin ya tashi da kashi 88 daga Naira biliyan 19.135 a watan Disamba 2022 zuwa naira biliyan 36.706 a farkon zangon shekarar 2023.

A jawabinsa a kan wannan nasarar da bankin ya samu a daidai wannan lokacin, shugaban Bankin, Mista Hamid Joda, ya ce, wannan nasarar ya samu ne sakamakon sabbin hanyoyin gudanar da aiki na zamani tare da samar da kwararrun ma’aikata masu mu’amala da abokan huldarmu yadda ya kamata.

Ya kara da cewa, wannan nasarar yana nuna cewa, aiki tukuru na da rabarsa kamar yadda muka tsayu a tsawon shekara uku. Babban burinmu shi ne abokan huldarmu, muna kuma kokarin gamsar da su ta hanyar amfani da dukkan kokarinmu don bayyana wa duniya cewa sune a gabanmu, mun dauki hanyar gudanar da harkokin banki ba tare da ruwa ba.

A takaitaccen jawabinsa, daya daga cikin wanda suka kirkiro da bankin, Mista Sherif Idi, ya danganta nasarar da suka samu ga masu hannun jari da abokan huldar bankin, ya kuma kara da cewa, “Muna godiya ga abokan huldar mu da masu hannun jarinmu wadanda sune suke zaburar da mu a nasarar da muke samu zuwa yanzu.

“Ina mai tabbatar muku da cewa, hukumar gudanarwa TAJBank da ma’aikatanta za su ci gaba da kare bukatun ku a dukkan harkokin bankin saboda yadda muka muhimmantar da ku”, in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

sallah
Tattalin Arziki

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida

October 11, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho

October 10, 2025
An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 
Tattalin Arziki

An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

October 10, 2025
Next Post
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Kama Hanyar Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba A Yankin Tsaunin Himalaya

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Kama Hanyar Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba A Yankin Tsaunin Himalaya

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
NAWIA

Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

October 16, 2025
Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

October 16, 2025
Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

October 16, 2025
Tinubu

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.