• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hutun Cikar Sin Shekaru 74 Ya Nuna Ci Gaban Da Kasar Ta Samu Da Wadatar Al’ummarta

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

Yanzu haka al’ummar kasar Sin suna hutu mai tsawo na kwanaki 8 da ya hada da hutun bikin tsakiyar kaka da kuma na zagayowar ranar kafuwar Jamhuriyar Jama’ar kasar Sin, wadda a bana ake cika shekaru 74.

Wani abu da kan burge ni da al’ummar Sinawa shi ne, kishin kasa. Yadda a birnin Beijing kadai mutane kusan 300,000 suka yi tattaki zuwa dandalin Tiananmen a ranar Lahadi da safe domin murnar ranar kafuwar kasar, ya burge ni ainun. Kuma ba birnin Beijing kadai ba, har ma dukkan sassan kasar da ma al’ummomin Sinawa dake ketare, su kan gudanar da bukukuwa domin zuwan wannan rana, lamarin dake nuna matukar kaunarsu da kishinsu ga kasar, har ma da ci gaban da ta samu.

  • Kasar Sin Ta Zama Abar Koyi Ga Goyon-Bayan Hadin-Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
  • Somaliya Da ATMIS Sun Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Tsakiyar Kasar

Haka kuma, wannan lokacin hutu ya kara tabbatar da ci gaban da kasar Sin ta samu tare da farfadowar harkokin yau da kullum bayan mummunar annobar da ta tsayar da kusan komai a duniya. Zan iya cewa, farfadowar harkokin ya samo asali ne daga jajircewar hukumomin kasar da shugabanci na gari da kuma kaifin basirar raya ta. Idan muka dauki lardin Hunan dake kudancin kasar Sin a matsayin misali, tafiye-tafiyen da aka yi da suka zarce miliyan 2.7 zuwa wuraren bude ido sama da 950 a ranar Asabar kadai, ya samar da kudin shigar da ya kai yuan miliyan 370, kwatankwacin dala milyan 50.7, wanda ya nuna karuwar kaso 49.1 akan na bara. Wannan ya kara tabbatar min da matakin kasar Sin na kokarin bunkasa tattalin arzikinta a cikin gida. Kasar Sin ta zabarwa kanta wata kyakkawar hanyar raya kanta cikin aminci da lumana.

Bugu da kari, wadannan tafiye-tafiye da yadda Sinawa ke murna, ya nuna cewa, kasar Sin ta yi namijin kokari wajen ganin al’ummarta na rayuwa cikin jin dadi da aminci da wadata kuma cike da tsaro.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba
Daga Birnin Sin

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
Next Post
Juyin Mulki: An Sake Bude Makarantu A Nijar Bayan Wata 3

Juyin Mulki: An Sake Bude Makarantu A Nijar Bayan Wata 3

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.