• English
  • Business News
Monday, July 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Halin Da Birnin Maiduguri Ya Tsinci Kansa A Ciki

by Muhammad Maitela and Bello Hamza
11 months ago
in Manyan Labarai
0
Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Halin Da Birnin Maiduguri Ya Tsinci Kansa A Ciki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ballewar Madatsar Ruwan Alau da ke karamar hukumar Konduga ta Jihar Borno ta jawo mummunan ambaliyar ruwan da ta mamaye gidajen jama’a tare da haifar da asarar dukiya mai dimbin yawa a Maiduguri, babban birnin Jihar Borno.

Haka zalika ambaliyar ta malale gidan ajiye namun daji (Zoo), wanda hakan ya jawo namun dajin fantsama cikin gari, wasu kuma suka mutu a ruwa.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Matafiya A Babbar Hanyar Gusau-Funtua
  • Kasar Sin Za Ta Zurfafa Hadin Gwiwa Da Sauran Kasashe A Bangaren Tsaron Intanet

A ranar Litinin gwamnatin jihar ta gargadi mazauna unguwanni masu makwabtaka da Gidan Namun Dajin da ke unguwar Sanda Kyarimi su gaggauta ficewa daga gidanjensu domin kauce wa hatsarin farmakin dabbobin.

Jama’a da dama a birnin Maiduguri sun tabbatar wa da LEADERSHIP Hausa cewa ambaliyar ruwan ta nutsar da gidajensu tare da ofisoshin gwamnati. Haka nan ruwan bai kyale fadar Shehun Borno ba tare da sauran muhimman wurare na birnin.

Bugu da kari, al’ummar da ke zaune a wasu unguwannin birnin Maiduguri sun bayyana karin fargabar irin yadda namun dajin suka fantsama cikin garin; wadanda suka hada da macizai, kadoji, mugun dawa, da sauran dabbobin masu hatsari.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

Wasu bayanai sun bayyana fargabar cewa ambaliyar ruwan ta kashe wasu da dama daga cikin dabbobin, irin su zakunan da suka tsufa kana wasu zakunan tare da jiminai sun tsere, duk da har zuwa lokacin hada wannan rahoto ba a samu wani rahoto na ta’asar da namun dajin da suka tsere suka yi wa al’ummar birnin ba.

Ambaliyar ta fara ce tun daga karshen mako kadan-kadan kafin daga bisani ta yi kamari a ranar Talata biyo bayan fashewar Madatsar Ruwan ta Alau. Unguwannin da al’amarin ya fi shafa sun hada da Fori, Galtimari, Gwange, Bulabulin, da tashar Bama.

Sauran unguwannin da ambaliyar ta malale a birnin na Maiduguri sun hada da London Ciki, Gidan Danbe, Zara Plaza, Lagos Street, Abbaganaram, Kofa, Budum, Kalari, Shehuri, Shehuri North, da kuma Post Office na Rukunin Gidajen Dikwa.

Har ila yau, ambaliyar ta mamaye gidaje, manyan hanyoyin mota da gadoji wanda kawo lokacin hada wannan rahoto ba a iya kiyasta yawan gidanjen da abin ya shafa ba, ballantana asarar da ta jawo.

Wasu rahotanni daga kafafen yada labarai daban-daban sun bayyana cewa akalla mutune 200,000 zuwa 500,000 ambaliyar ta shafa. Tarihi ya nuna cewa an taba yin makamanciyar ta kimanin shekaru 30 da suka gabata, a watan Satumbar 1994, a daidai irin wannan lokacin na bana, duk dai a sanadiyyar ballewar madatsar ruwan ta Alau.

Sai dai barnar da ake ganin ambaliyar wannan karon ta haifar ta dara ta wancan karon.

A cikin wata sanarwa da Gwamnatin Jihar Borno ta fitar, mai dauke da sa hannun Kwamishinan Yada Labaru da Al’amurran Cikin Gida, Farfesa Usman Tar, da safiyar ranar Talata, gwamnatin ta gargadi mazauna wasu unguwanni a birnin na Maiduguri su gaggauta kaurace wa yankunan da ambaliyar ta shafa.

“Saboda kwararowar ruwan ta saba da yadda aka saba, muna kira ga daukacin jama’ar da ke zaune a wuraren da ambaliyar ke yin barazana, a matsayin matakin kare rayukan al’umma da dukiyoyinsu cikin gaggawa, su kaurace wa wuraren da abin ya shafa.

“Har ila yau mun dauki wannan matakin ne bisa ga bayanan da muka samu na fashewar Madatsar Ruwan Alau, kuma ya tunkaro cikin gari, baya ga lalata gonaki da ya yi.” In ji sanarwar.

Tuni dai gwamatin tarayya ta mika sakon jaje ga al’ummar Jihar Borno a kan faruwar wannan ibtila’in, inda mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya kai ziyarar gani ido sassan da abin ya shafa.

Da yake jawabi a wani matsugunin mutanen da abin ya shafa, Shettima ya ce, gwamnati ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen aiko da dukkan taimakon da ake bukata na ragewa al’umma radadin da suke fuskanta. Ya kuma yaba wa kokari Gwamna Zulum a kan yadda ya dauki matakin gaggawa wajen tura hukumomin bayar da agaji na jihar wuraren da ake bukatar taimako.

Gwamatin jihar dai ta ayyana cewa, fiye da kashi 80 na al’ummar jiihar ambaliyar ta shafa, ta kuma ce, bukaci jama’a sus a ido tare da kula da sosai wajen kiyaye lafiyarsu musamman bisa silalewar namun daji zuwa cikin gari.

Ambaliyar dai ta tilasta rufe muhimman wurare a jihar da suka hada da Jami’ar Maiduguri, da kuma wata cibiyar koyar da matasa da ke kusa da Jami’ar. A wata sanarwa da magatakardar Jami’ar, Fatima Muhammad Audu, ta fitar, ta ce an yi haka ne domin kare rayukan dalibai da ma’aikata musanmma ganin ana iya samun barkewar cututtuka da sauran matsaloli skamakom wannan ambaliyar, “Kuma ba ma son a samu wata mastalar da za ta fi karfimu a nan gaba, ana sa ran sake bude makaratar ne a ranar 16 ga watan Satumba 2024 in Allah ya yarda’ in ji ta.

Haka kuma gwamatin JIhar ta umarci a kulle dukkan makarantun gwamnati da na masu zama kansu a fadin jihar har zuwa ranar 23 ga watan Satumba 2024 saboda wanan ibtila’in ambaliyar da aka fuskanta.

Da yake tofa albarkacin bakinsa, shugaban wata kungiya mai zama kanta a Jihar Borno mai suna Network of Cibil Society Organisations’ Kwamrade Bulama Abiso, ya nemi a tabbatar da samar da tallafi issashe ga wadanda ibtila’in ya shafa, domin a cewarsa, iyalai da dama musamman mata da kananan yara sun shiga halin ni’yasu sakamakon ambaliyar.

A halin da ake ciki dai tuni, Gwamatin Jihar Boro ta bude sansanin ‘yan gudun hijira na Bakassi da ke Maiduguri domin tsugunar da wadanda ambaliyar ta shafa.

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa (NEMA) ta bayyana cewa, ambaliyar ruwan da ta auku a baya-bayan nan a fadin Tarayyar Nijeriya kafin wannan ta Maiduguri, ta lalata amfanin gona kimanin fadin kadada 16,488 a fadin jihohi 27. Bugu da kari, sama da gidaje 32,000 ne al’amarin ya shafa tare da jefa sama da mutum 227,000 cikin mawuyacin hali.

A nashi bangare, karamin ministan noma da bunkasa abinci a Nijeriya, Sanata Abdullahi Sabi Aliyu, ya bayyana cewa kusan kashi 51 cikin dari na amfanin gona a fadin Nijeriya na fuskantar barazanar ambaliya a 2024. A daya bangaren kuma, ministan ya yi gargadin cewa ambaliyar da ke ci gaba da gudana, za ta kawo babbar cikas da kuma gibi ga kokarin samar da abinci a kasar nan.

Mutanen garin Maiduguri da ambaliyar ruwa ta tarwatsa su bayan da dam din Alau ya fashe a halin yaznu sun fara komawa gidajen su bayan da ruwan ya fara janyewa a hankali a wasu wuraren.

Rahoton kamfanin dillancin labarann Nijeriya ya nuna cewa, mutanenn da suka kwana a waje duk sun kosa su koma gidajen su domin ganin irin barnar da ambaliyar ta yi musu.

Wuraren da ruwan ya fara lafawa sune, Gwange da Gomari. Amma kuma wasu wurare da dama duk ruwa ya mamaye su, al’umma ba za su iya shiga ba a yanzu.

A halin yanzu kugiyar majalisar dinki duniya masu kula da bayar da agaji ta ce, fiye da mutum 239,000 ambaliyar ruwan ta shafa a ganin Maidugri. Mutum 50,000 sun samu mafaka a sansanin ‘ya gudun hijira na Muna.

Ambaliyar ruwa ta haifar da cikas ga samar da wutar latarki da ruwa famfo a sasan garin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ambaliyar RuwaBornoMaiduguri
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ta’addancin ‘Yan Ta’adda A Kan Sarakuna

Next Post

Shirin X Space Na LEADERSHIP: Tabbas Gwamnatin Kano Ta Hau Turbar Bunkasa Ilimi – Mahalarta

Related

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

2 hours ago
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Rasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi
Da ɗumi-ɗuminsa

SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

4 hours ago
Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja
Manyan Labarai

Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

6 hours ago
Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno
Manyan Labarai

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

8 hours ago
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

1 day ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

2 days ago
Next Post
Dakatar Da Albashin Sabbin Ma’aikatan Kano: Nakasassu Sun Shiga Tsaka-mai-wuya —Zango

Shirin X Space Na LEADERSHIP: Tabbas Gwamnatin Kano Ta Hau Turbar Bunkasa Ilimi – Mahalarta

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

July 28, 2025
Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

July 28, 2025
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

July 28, 2025
Gwamnatin Sakkwato Ta Ƙaddamar Da Sababbin Motoci 30, Don Bunƙasa Sha’anin Sufuri A Jihar

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

July 28, 2025
Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021

Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021

July 28, 2025
Sin Ta Samar Da Manyan Manhajojin AI Sama Da 1500

Sin Ta Samar Da Manyan Manhajojin AI Sama Da 1500

July 28, 2025
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Rasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi

SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

July 28, 2025
Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

July 28, 2025
SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai

SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai

July 28, 2025
Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

July 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.