ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin X Space Na LEADERSHIP: Tabbas Gwamnatin Kano Ta Hau Turbar Bunkasa Ilimi – Mahalarta

by Naziru Adam Ibrahim
2 years ago
Kano

Masu ruwa da tsaki a fannin ilimi sun yaba wa kokarin Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf, wajen inganta bangaren duba da gagarumar nasarar da ake samu biyo bayan ayyana dokar ta baci da ya yi a fannin ilimin jihar.

Sun bayyana hakan ne cikin shirin tattaunawa da LEADERSHIP ta shirya a shafinta na X da akafi sani da twitter inda masu ruwa da tsakin suka yaba da da matakan da gwamnatin ke dauka.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Matafiya A Babbar Hanyar Gusau-Funtua
  • Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Birnin Baoji Na Lardin Shaanxi Da Birnin Tianshui Na Lardin Gansu

Cikin jawabinta, babbar hadimar Gwamna Abba Kabir Yusuf, kan ilimin Mata  Hajiya Yesmin Mukhtar, ta ce gwamnan ya gyara makarantu da dama da ke cikin halin kaka-ni-ka-yi tare da bude wasu da a da can baya an nuna musu halin ko in kula.

ADVERTISEMENT

Sauran ci gaban da aka samu kamar yadda sauran masu tofa albarkacin bakinsu irin su tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kaduna, Farfesa Usman Moddibo da mai mallakar shafin Arewa Twitter, Malam Abdullahi Nasarawa suka bayyana, akwai kaddamar da manyan ayyuka na gyaran makarantu da kuma inganta kwazazon malamai.

Duk sun yaba wa gwamnatin jihar kan wasu daga cikin jiga-jigan kokarinta na inganta harkar ilimin irin su ware kaso 29 na kasafin jihar ga bangaren ilimi da diban malamai fiye da 5,600 da biyan kudaden jarrabawar WAEC da NECO ga dalibai da bude cibiyoyin samun ilimin zamani na na’ura mai kwakwalwa.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

Sai dai sun ce duk da haka akwai sauran aiki a gaba wanda idan aka mayar da hankali tabbas za a yi nasarar har karshe.

Shi ma kwamishinan ilimi na Jihar Kano, Alhaji Umar Haruna Doguwa ya bayyana bukatar yaba kokarin da gwamnatin ke yi ta hanyar ba ta duk wani hadin kai da take bukata don samun nasara.

Zuwa yanzu dai, daga cikin gagarumin kokarin da take yi, Gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta fitar da fiye da Naira Biliyan 2.7 domin gina ajujuwa 176 da ofisoshi 88 a sassan kananan hukumomin jihar 44.

Kano
Naziru Adam Ibrahim
+ postsBio
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    Shugaba Tinubu Ya Isa Nairobi Domin Halartar Taron Tattalin Arzikin Nahiyar Afirka
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    Gwamnatin Filato Ta Kwato Kadarorin Jihar Da Aka Wawashe
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    DSS Da Jami’an Kotu Sun Kori Ƴan Jarida Daga Ɗakin Shari’a A Abuja
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    Zaɓen 2027: APC Na Iya Hana Mu Yin Kamfen – Buba Galadima

MASU ALAKA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
Ilimi

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

May 31, 2026
Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
Ilimi

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

May 30, 2026
Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
Next Post
Ƴan Bindiga Sun Tare Hanyar Zamfara, Sun Sace Matafiya 150

Ƴan Bindiga Sun Tare Hanyar Zamfara, Sun Sace Matafiya 150

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.