• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Idan Aka Fatattaki ‘Yan Ta’adda Daga Zamfara Duk Arewa Za Mu Samu Sauki – Gwamna Dauda

by Bello Hamza
1 year ago
in Labarai
0
Maulidi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal ya koka ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a kan karuwar harkokin ta’addanci a Jihar Zamfara, yana mai cewa, in har aka samu nasarar fattakar ‘yan ta’adda a Jihar Zamfara tamkar an kore su ne daga yankin arewa gaba daya.

Gwamnan ya bayyana haka ne a tattaunawarsa da manema labarai a fadar shugaban kasa da ke Abuja ranar Talata. Ya kuma kara da cewa, barin ‘yan ta’adda na cin karensu babu babbaka a yankin Zamfara yankin arewa gaba daya zai ci gaba da kasancewa a cikin hadari.

  • Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Da Takwaransa Na Kasar Kazakhstan Sun Mika Sakwannin Murnar Kaddamar Da “Shekarar Yawon Bude Ido Ta Kazakhstan” A Sin
  • Gwamna Dauda Lawal Ya Gana Da Ministan Ruwa Domin Kammala Ayyukan Ruwa A Zamfara

Daga na Gwamna Lawal ya kuma ce, “A yau a mastayina na Gwamnan Jihar Zamfara na zo fadar shugaban kasa (villa) inda na gana da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu domin na yi masa bayanin irin matsalolin da muke fuskanta na rashin tsaro a Jihar Zamfara, wanda kuma tattunawar tamu ta yi amfani kwarai da gaske, domin ya bani tabbacin cewa, da ikon Allah zai yi duk abin da zai yi ya taimaka mana a Jihar Zamfara don mu samu sauki. Saboda idan ka duba yanzu duk matsalolin tsaro da ake samu yanzu a kusa yankin arewa gaba daya abubuwa ne da suke tasowa daga Zamfara, saboda haka idan aka yi abin da ya kamata a yankin Zamfara kusan dukka yankin arewa za a samu sauki”
Ya kuma bayyana cewa. “Na ji dadin wannan tattauanwar na kuma yi farin ciki sosai. Haka kuma ya gamsu da dukkan bayanin da na yi masa a ka matsalolin da muke fuskanta a Zamfara na mastalar tsaro. Wasu matsalolin da na yi masa bayani a kai da can bai san dasu ba, amma yau ya san kusan komai da ke faruwa a wannan jihar ta mu”.

Tun da ya dare karagar mulkin jihar ne, Gwamna Lawal yake fadi tashin ganin an samu zaman lafiya a jihar Zamfara. Cikin matakan da ya dauka akwai da kafa rundunar Askarawan Zamfara wanda aka shirya za su yi aiki kafada da kafada da jami’an tsaro don fatattakar ‘yan bindiga.

A kwanan nan ma ya ziyarci shugaban rundunar tsaro Janar CG Musa inda ya nemi a kara yawan sojojin da ke aiki a Zamfara don dakile ayyukan ‘yan ta’adda.

Labarai Masu Nasaba

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

IFAD Da Gwamnatin Tarayya Sun Yi Hadaka Don Bunkasa Aikin Noma A Arewa

Next Post

Minista Ya Bayyana Cikakken Dalilin Kafa Askarawan Kare Ma’adanai

Related

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi
Labarai

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

2 hours ago
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

5 hours ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

6 hours ago
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 
Labarai

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

6 hours ago
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

7 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

9 hours ago
Next Post
Minista Ya Bayyana Cikakken Dalilin Kafa Askarawan Kare Ma’adanai

Minista Ya Bayyana Cikakken Dalilin Kafa Askarawan Kare Ma’adanai

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.