ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Bayyana Cikakken Dalilin Kafa Askarawan Kare Ma’adanai

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Ma'adanai

Ministan ma’adanai, Dele Alake ya karbi bakuncin rukuni na farko na Askarawan kare ma’adanai da aka kafa kwanan nan domin su yi aikin kare wuraren da ake hakar ma’adanai a sassan kasar nan.

An kafa Askarawan ne a karkashin jagorancin shugaban hukumar tsaron farin kaya (NSCDC), Abubakar Audi. A ranar 1 ga watan Maris ne Ministan cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo ya kaddamar da rundunar don su yi aikin kawo karshen masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a sassan Nijeriya, wanda hakan ake sa ran zai inganta kudaden shiga a bangaren tattalin arzikin Nijeriya.

  • Ba Ka Da Aiki Sai Yin Barci A Abuja – Martanin Ɗan El-Rufai Ga Uba Sani
  • El-Rufai Ya Jibge Min Bashin $587 Da Biliyan 85 A Kaduna – Uba Sani

Kaddamar da dakarun ya yi daidai da bikin ranar da majalisar dinkin duniya ta ware don bikin ranar kula da hakkin fararen hula a duniya, wanda aka yi a Abuja.
Ma’aikatar ma’adanai ne ta su kula da ayyukan Askarawan.

ADVERTISEMENT

An shirya cewa, za a tattaro dakarun ne daga jihohin tarayyar Nijeriya da babban birnin tarayya Abuja inda a halin yanzu aka kafa runduna mai mutum 60.

Alake ya umarci dakarun su tabbatar da sun kawo karshen sace-sace da ayyukan ta’addanci da ke faruwa a wuraren hakar ma’adanai a sassan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Minista Alake ya kuma yaba wa Minista Olubunmi-Ojo a kan yadda ya tsayu na ganin an samu nasarar kafa rundunar.

“An kaddamar da Askarawan ne tare da hadin gwiwar ministan cikin gida don kare wuraren hakar ma’adanai, ta haka za a tabbatar da cin gajiyar albarkatun ma’adanai da Allah ya shinfida a sassan Nijeriya.Wannan kuma na daga cikin shirye-shiryen da Shugaba Tinubu ya yi na bunkasa bangaren hakar ma’adanai na Nijeriya, ”Kamar yadda Segun Tomori mai ba Minista Alake shawara a kan harkokin yada labarai ya bayyana a sanarwa da ya raba wa manema labarai.

“Ina mai farin cikin sanar da al’umma cewa, an kafa dakarun ne don tsaftace wuraren hakar ma’adanai daga matsalar tsaro, mun kuma samu nasarar kafa rukuni na farko na jami’an da za su yi wannan aikin kamar yadda muka kaddamar a yau.”

Ma'adanai
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
Bassirou Diomaye Faye: Daga Kurkuku Ya Zama Shugaba Mafi Karancin Shekaru A Afirka

Bassirou Diomaye Faye: Daga Kurkuku Ya Zama Shugaba Mafi Karancin Shekaru A Afirka

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.