• English
  • Business News
Friday, August 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Idan Buhari Bai Taimaki Tinubu Ba, Bai Kamata Ya Yake Shi Ba Don Ya Taimake Shi —Rarara

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
in Siyasa
0
Idan Buhari Bai Taimaki Tinubu Ba, Bai Kamata Ya Yake Shi Ba Don Ya Taimake Shi —Rarara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shahararren mawakin siyasar nan na ƙasar Hausa kuma mawakin shugaba Buhari, Dauda Abdullahi Kahutu Rarara, ya gargaɗi shugaban ƙasa Buhari da kar ya sake ya yaki, Bola Ahmad Tinubu, saboda ya taimaki shi a lokacin da yake buƙatar taimako.

Rarara ya bayyana haka cikin wani faifon bidiyo da ya karade kafafen yada labarai na zamani dangane da batun da wasu ‘ya ‘yan jam’iyyar APC ke cewa, Bola Ahmad Tinubu, ya yi wa shugaban ƙasa Buhari gorin taimako.

  • 2023: Tinubu Ne Mafi Dacewa Da Zama Shugaban Kasa —’Yan Kudu Maso Yamma
  • Babu wata Yarjejeniya Da Aka Gindaya Cewa Za A Ba Tinubu Shugaban Kasa Bayan Buhari -Yerima

Wannan magana da Bola ya yi da alama bata yi wa wasu daga cikin magoya bayan shugaba Buhari daɗi ba, saboda suna ganin babu wani dalili da zai sa, Bola Ahmad Tinubu, ya share wuri yana maganganu masu kama da suka ta kai -tsaye ga shugaba Buhari.

Inda har suke ganin kamar Bola Ahmad Tinubu yana ƙoƙarin wuce makaɗi da rawa, saboda neman mulki har yana ƙoƙarin cin fuskar shugaban ƙasa Muhammad Buhari.

Mawakin wanda ya ce Bola Ahmad Tinubu ya taimaki shugaban ƙasa, Muhammad Buhari, kuma ko shi Buhari ba zai ƙaryata hakan ba, ya ce har na kusa da Buharin ma sun san haka.

Labarai Masu Nasaba

An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

An ruwaito shugaban jam’iyyar APC na ƙasa Sanata Abdullahi Adamu yana cewa za su iya ɗaukar mataki akan Bola Tinubu dangane da wadancan kalamai na shi.

Shi kuwa mawakin na Buhari Dauda Kahutu Rarara ya ce wasu da ke ɗaukar wannan magana da zafi da yawan su ‘yan ‘good evening ne’ wato dai ‘yan ta more ne, amma ba su san da wancan zancen ba.

” An samu wani lokaci da Buhari ke buƙatar taimako kuma akwai ‘yan arewa da suke da halin da za su taimaka masa amma suka ƙi taimakonsa sai shi Bola Tinubu ɗin ne ya taimaki Buhari kuma ya samu abinda yake so” in ji shi.

Saboda haka a cewar Rarara babu wanda ya isa ya ce Bola Tinubu bai taimaki Buhari ba kuma shi Buharin ya sani, ya ce hatta mu ɗin nan mun sani.

Ya kara da cewa shi Bola Tinubu abokin siyasar Buhari ne, ya taimaki Buhari ya zama ɗan takara kuma yai zo ya taimaka aka kafa gwamnati da shi.

A cewar Rarara baban abinda zai yi na nunawa arewa dattako shi ne, ko dai ya goyi bayan Tinubu ko kuma ya bada dama ga kowa da kowa ya shiga zaɓen fidda gwani wanda Allah ya ba shikenan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2023APCBuhariRararaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Al’adun Duanwu Na Kasar Sin Dake Da Tarihin Fiye Da Shekaru 2000

Next Post

Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Kasa Na Ranar Muhalli Ta Shekarar 2022

Related

An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano
Labarai

An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano

11 hours ago
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

3 days ago
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

3 days ago
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027
Siyasa

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

5 days ago
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027
Siyasa

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

6 days ago
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10
Siyasa

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

6 days ago
Next Post
Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Kasa Na Ranar Muhalli Ta Shekarar 2022

Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Kasa Na Ranar Muhalli Ta Shekarar 2022

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

August 15, 2025
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

August 15, 2025
Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

August 15, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Babu Dalilin Da Zai Sa ‘Yan Nijeriya Su Yi Talauci – Tinubu

August 15, 2025
Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

August 15, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Ya Kamata Japan Ta Martaba Tarihi

Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Ya Kamata Japan Ta Martaba Tarihi

August 15, 2025
Akwai Bukatar Samar Da Sauyin Zaman Lafiya Mai Dorewa A Duniya — Maryam Bukar

Akwai Bukatar Samar Da Sauyin Zaman Lafiya Mai Dorewa A Duniya — Maryam Bukar

August 15, 2025
Sin Ta Soki Lamirin Amurka Dangane Da Wanke Japan Daga Laifukan Da Ta Tafka Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Sin Ta Soki Lamirin Amurka Dangane Da Wanke Japan Daga Laifukan Da Ta Tafka Yayin Yakin Duniya Na Biyu

August 15, 2025
UBEC Ta Kaddamar Da Makarantun Zamani 21 A Sassan Nijeriya

UBEC Ta Kaddamar Da Makarantun Zamani 21 A Sassan Nijeriya

August 15, 2025
Firaministan Sin Ya Bukaci A Zage Damtse Wajen Bude Sabon Babin Gina Wayewar Kai Ta Fuskar Kare Muhallin Halittu A Sabon Zamani

Firaministan Sin Ya Bukaci A Zage Damtse Wajen Bude Sabon Babin Gina Wayewar Kai Ta Fuskar Kare Muhallin Halittu A Sabon Zamani

August 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.