ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu wata Yarjejeniya Da Aka Gindaya Cewa Za A Ba Tinubu Shugaban Kasa Bayan Buhari -Yerima

by Muhammad
4 years ago
Babu

Tsohon gwamnan jihar Zamfara, Sanata Ahmad Sani Yerima, ya ce babu wata yarjejeniya tsakanin jam’iyyar APC da Ahmad Tinubu, na ba shi takarar shugaban kasar nan bayan mulkin shugaba Muhammadu Buhari.

Yerima, wanda kuma dan takarar shugaban kasa ne a jam’iyyar APC mai mulki, ya bayyana hakan a cikin shirin siyasa na Trust Tv, Daily Politics, a daren Juma’a.

  • Kwamitin tantance ‘Yan Takarar Shugaban Kasa Na APC Ya Yi Watsi Da ‘Yan Takara 10 Cikin 23
  • 2023: Buhari Zai Gana Da Masu Ruwa Da Tsaki Don Fitar Da Magajinsa Gabanin Taron APC

Tinubu, yayin da yake zantawa da wakilan jam’iyyar a jihar Ogun a ranar Alhamis, ya ce lokaci ya yi da zai zama shugaban Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Tsohon gwamnan jihar Legas ya kuma bayyana yadda ya goyi bayan Buhari a takararsa ta shugaban kasa tare da ba da ba Osinbajo mukamin mataimakin shugaban kasa, wanda shi ma a halin yanzu ke zawarcin mukamin shugaban kasa bayan ya gama mataimakin shugaban kasa karo na biyu.

Idan zamu iya tunawa, Jam’iyyar Tinubu, (ACN) ta narke wuri guda da sauran Jam’iyyu a watan Fabrairun 2013, tare da (CPC) da (ANPP) – da kuma wani bangare na (APGA) domin kafa jam’iyyar APC tare da Buhari daga jam’iyyar CPC aka ba shi damar tsayawa takarar babban mukami.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

An yi imanin cewa akwai yarjejeniyar da ACN ta yi na cewa za ta fitar da dan takarar shugaban kasa na gaba bayan mulkin Buhari.

Sai dai Yerima ya ce babu wani rahoto da ke nuna an kulla irin wannan yarjejeniya da jam’iyyar.

“Babu wata yarjejeniya da t tabbatar da haka, a lokacin wanene shugaban jam’iyyar? Da farko muna da Cif Bisi Akande, daga baya kuma, muna da John Oyegun, kuma a yau muna da Sanata Abdullahi Adamu, muna da [Mai Mala] Buni a cikin tafiyar da dai sauransu.

“To, ko Cif Bisi Akande ne ya zauna da wasu mutane? Duk wani hukunci da aka dauka a wajen tsarin jam’iyyar ba a amince da shi ba. Jam’iyyar tana da kwamitin ayyuka na kasa, jam’iyyar kuma tana da abin da muke kira NEC kuma akwai bangaren yanke shawara gaba daya wato babban taron kasa.

Ya ci gaba da cewa, “Duk hukuncin da ba a dauka a cikin tsarin jam’iyyar ba, ba hukunci ba ne. Ba za ku iya samun fahimta da mutum ba kuma ku ce ‘hakan zai faru. Idan jam’iyya tana son yanke shawara, ko dai kwamitin ayyuka na kasa ne, ko hukumar zabe ta yanke.

“Idan Yarjejeniyar ta yanke shawara, ba za a iya canza ta ba. Amma za a iya sake duba yanke shawara bisa kowane yanayi. Ko da akwai wannan fahimtar, yanayin yau na iya bambanta da yadda yake lokacin da aka cimma wannan fahimtar. ”

Jam’iyyar APC ta tsayar da ranar 6 ga watan Yuni a matsayin ranar babban taronta a birnin tarayya Abuja, inda za ta zabi dan takararta na shugaban kasa a zaben 2023.

Babu
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Mene Ne Bambancin Wadannan Ruwan Guda Biyu Masu Fitowa Daga Gaban Mace?

Mene Ne Bambancin Wadannan Ruwan Guda Biyu Masu Fitowa Daga Gaban Mace?

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.