ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu wata Yarjejeniya Da Aka Gindaya Cewa Za A Ba Tinubu Shugaban Kasa Bayan Buhari -Yerima

by Muhammad
4 years ago
Babu

Tsohon gwamnan jihar Zamfara, Sanata Ahmad Sani Yerima, ya ce babu wata yarjejeniya tsakanin jam’iyyar APC da Ahmad Tinubu, na ba shi takarar shugaban kasar nan bayan mulkin shugaba Muhammadu Buhari.

Yerima, wanda kuma dan takarar shugaban kasa ne a jam’iyyar APC mai mulki, ya bayyana hakan a cikin shirin siyasa na Trust Tv, Daily Politics, a daren Juma’a.

  • Kwamitin tantance ‘Yan Takarar Shugaban Kasa Na APC Ya Yi Watsi Da ‘Yan Takara 10 Cikin 23
  • 2023: Buhari Zai Gana Da Masu Ruwa Da Tsaki Don Fitar Da Magajinsa Gabanin Taron APC

Tinubu, yayin da yake zantawa da wakilan jam’iyyar a jihar Ogun a ranar Alhamis, ya ce lokaci ya yi da zai zama shugaban Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Tsohon gwamnan jihar Legas ya kuma bayyana yadda ya goyi bayan Buhari a takararsa ta shugaban kasa tare da ba da ba Osinbajo mukamin mataimakin shugaban kasa, wanda shi ma a halin yanzu ke zawarcin mukamin shugaban kasa bayan ya gama mataimakin shugaban kasa karo na biyu.

Idan zamu iya tunawa, Jam’iyyar Tinubu, (ACN) ta narke wuri guda da sauran Jam’iyyu a watan Fabrairun 2013, tare da (CPC) da (ANPP) – da kuma wani bangare na (APGA) domin kafa jam’iyyar APC tare da Buhari daga jam’iyyar CPC aka ba shi damar tsayawa takarar babban mukami.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

An yi imanin cewa akwai yarjejeniyar da ACN ta yi na cewa za ta fitar da dan takarar shugaban kasa na gaba bayan mulkin Buhari.

Sai dai Yerima ya ce babu wani rahoto da ke nuna an kulla irin wannan yarjejeniya da jam’iyyar.

“Babu wata yarjejeniya da t tabbatar da haka, a lokacin wanene shugaban jam’iyyar? Da farko muna da Cif Bisi Akande, daga baya kuma, muna da John Oyegun, kuma a yau muna da Sanata Abdullahi Adamu, muna da [Mai Mala] Buni a cikin tafiyar da dai sauransu.

“To, ko Cif Bisi Akande ne ya zauna da wasu mutane? Duk wani hukunci da aka dauka a wajen tsarin jam’iyyar ba a amince da shi ba. Jam’iyyar tana da kwamitin ayyuka na kasa, jam’iyyar kuma tana da abin da muke kira NEC kuma akwai bangaren yanke shawara gaba daya wato babban taron kasa.

Ya ci gaba da cewa, “Duk hukuncin da ba a dauka a cikin tsarin jam’iyyar ba, ba hukunci ba ne. Ba za ku iya samun fahimta da mutum ba kuma ku ce ‘hakan zai faru. Idan jam’iyya tana son yanke shawara, ko dai kwamitin ayyuka na kasa ne, ko hukumar zabe ta yanke.

“Idan Yarjejeniyar ta yanke shawara, ba za a iya canza ta ba. Amma za a iya sake duba yanke shawara bisa kowane yanayi. Ko da akwai wannan fahimtar, yanayin yau na iya bambanta da yadda yake lokacin da aka cimma wannan fahimtar. ”

Jam’iyyar APC ta tsayar da ranar 6 ga watan Yuni a matsayin ranar babban taronta a birnin tarayya Abuja, inda za ta zabi dan takararta na shugaban kasa a zaben 2023.

Babu
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Mene Ne Bambancin Wadannan Ruwan Guda Biyu Masu Fitowa Daga Gaban Mace?

Mene Ne Bambancin Wadannan Ruwan Guda Biyu Masu Fitowa Daga Gaban Mace?

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.