• English
  • Business News
Monday, September 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Idan Rana Ta Fito…

by yahuzajere
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Idan Rana Ta Fito…
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A bana ne, shawarar Ziri daya da hanya daya, shawarar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar a shekarar 2013 take cika shekaru 10 cif da kafuwa. Da farko dai shawarar ta mayar da hankali ne kan batun zuba jari a fannin ababen more rayuwa, da Ilimi, da gine-gine, da hanyoyin mota da layin dogo, da rukunin gidajen kwana, da tashoshin samar da wutar lantarki, da sauran muhimman fannoni da dan-Adam ke bukata a al’amuran rayuwar yau da kullum.

Alkaluma na nuna cewa, shawarar Ziri daya da hanya daya ta kasance tsarin da ya gudanar da ayyukan more rayuwa da zuba jari mafi girma a tarihi, inda ya shafi sama da kasashe 68, ciki har da kaso 65 cikin 100 na yawan al’ummar duniya, da kaso 40 cikin 100 na ci gaban GDPn duniya a shekarar 2017.

  • Angola Ta Yabawa Ingancin Sabon Filin Jirgin Sama Da Kamfanin Sin Ke Ginawa A Kasar

Shawarar Ziri daya da hanya daya, ta yi nasarar magance gibin ababen more rayuwa, kana tana da karfin bunkasar tattalin arziki a yankin Asiya da fasifik da yankunan tsakiya da gabashin Turai. Masana sun yi imanin cewa, shawarar tana da muhimmanci sosai wajen bunkasa alakar kasa da kasa.

Bugu da kari, shawarar, ta baiwa kasar Sin damar raba dabarun ci gaban ta da sauran kasashen Afirka masu tasowa, wanda hakan ya haifar da nasarar kammala layukan dogo, da titunan mota, da tashoshin jiragen ruwa da na sama, a birane da garuruwa a sassa daban-daban na kasashen Afirka da Asiya da ma sassan duniya, ayyukan da suke taka muhimmiyar rawa a fannin bunkasa ci gaban tattalin arziki da zamantakewar irin wadannan kasashe. Kuma sabanin yadda kasashen yamma ke zargi da ma neman bata sunanta, idan aka dubi ci gaban da nahiyar Afirka ke samu a fannin samar da ababen more rayuwa, za a fahimci irin taimako da shawarar take baiwa nahiyar. Hakika kasar Sin na samar da agaji irin wanda kasashen Afirka ke bukata.

Tun bayan da aka gabatar da shawarar, ya zuwa yanzu, kasar Sin ta yi aiki tare da kasashen da abin ya shafa, wajen zurfafa hadin gwiwar moriyar juna bisa ka’idar yin shawarwari mai zurfi, da ba da gudummawar hadin gwiwa, da samun moriyar juna, kana ta cimma nasarori masu tarin yawa. Bayanai sun nuna cewa, kasar Sin tana kokarin gina layukan dogo a kasashen nahiyar Asiya, da Turai, da arewacin Amurka, da kuma Afirka, wadanda suka zama shaidun aikin raya shawarar Ziri daya da hanya daya da kuma hadin gwiwa tsakanin kasa da kasa a wannan fanni.  Babu shakka, shawarar Ziri daya da hanya daya, ta zama wani babban dandalin hadin gwiwa na kasa da kasa mafi girma a duniya. Idan rana ta fito, tafin hannu ba ya rufe ta. (Ibrahim Yaya)

Labarai Masu Nasaba

AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

Shugaban Zimbabwe Ya Sauka Beijing Domin Halartar Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Babu Bukatar Taron Kolin Demokuradiyya Mai Haifar Da Fada Da Juna

Next Post

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Cote d’Ivoire

Related

AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci
Daga Birnin Sin

AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

47 minutes ago
Shugaban Zimbabwe Ya Sauka Beijing Domin Halartar Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan
Daga Birnin Sin

Shugaban Zimbabwe Ya Sauka Beijing Domin Halartar Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan

2 hours ago
Xi Ya Gabatar Da Jawabin Bude Taron Majalisar Shugabannin Kasashe Membobin Kungiyar SCO
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gabatar Da Jawabin Bude Taron Majalisar Shugabannin Kasashe Membobin Kungiyar SCO

3 hours ago
Antonio Guterres: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Sanin Ya Kamata
Daga Birnin Sin

Antonio Guterres: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Sanin Ya Kamata

5 hours ago
Firaministan Kasar Pakistan: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Pakistan: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Hangen Nesa

7 hours ago
Xi Jinping Ya Gana Da Narendra Modi 
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Narendra Modi 

1 day ago
Next Post
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Cote d’Ivoire

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Cote d’Ivoire

LABARAI MASU NASABA

Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

September 1, 2025
AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

September 1, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Da Ƙarin Kasafin Naira Biliyan 215.3 A Na 2025

September 1, 2025
Shugaban Zimbabwe Ya Sauka Beijing Domin Halartar Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan

Shugaban Zimbabwe Ya Sauka Beijing Domin Halartar Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan

September 1, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mata Da Yara A Zamfara

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mata Da Yara A Zamfara

September 1, 2025
Xi Ya Gabatar Da Jawabin Bude Taron Majalisar Shugabannin Kasashe Membobin Kungiyar SCO

Xi Ya Gabatar Da Jawabin Bude Taron Majalisar Shugabannin Kasashe Membobin Kungiyar SCO

September 1, 2025
NAPTIP Da Hisbah Sun Ceto Mata 12 Da Aka Yi Safararsu A Kano Zuwa Saudiyya

NAPTIP Da Hisbah Sun Ceto Mata 12 Da Aka Yi Safararsu A Kano Zuwa Saudiyya

September 1, 2025
Antonio Guterres: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Sanin Ya Kamata

Antonio Guterres: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Sanin Ya Kamata

September 1, 2025
Tinubu Ya Yi Adalci Ga Dukkan Yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ya Yi Adalci Ga Dukkan Yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

September 1, 2025
Firaministan Kasar Pakistan: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Kasar Pakistan: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Hangen Nesa

September 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.