• English
  • Business News
Monday, June 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

by Sulaiman
3 hours ago
in Labarai
0
Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya bayyana cewa gwamnatinsa ba ta karbi lamuni ko rance domin gudanar da ayyukan kawo sauyi da ake yi a duk faɗin jihar ba, kuma duk da haka yana da isassun kuɗi a ausun jihar.

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne a yayin tattaunawa da ya yi da wasu Editoci a ofishin sa da ke Gusau, babban birnin jihar a ranar Laraba, inda ya yi cikakken bayani kan nasarorin da gwamnatin sa ta samu tun hawan sa mulki kusan shekaru biyu da suka gabata.

  • Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?
  • Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

Gwamna Lawal ya bayyana manyan ci gaban da aka samu a bangarori masu muhimmanci da suka haɗa da tsaro, ilimi, kiwon lafiya, ababen more rayuwa, da ƙarfafa tattalin arziki.

 

Labarai Masu Nasaba

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

Yakin Iran Da Isra’ila Ya Haifar Da Tashin Farashin Litar Man Fetur A Nijeriya

Ya nanata cewa nasarar da aka samu ya zuwa yanzu ta samo asali ne sakamakon kyawawan tsare-tsare, ingantaccen jagoranci, da kuma kula da albarkatu.

 

Gwamnan ya bayyana cewa an samu ci gaba sosai a harkar tsaro a jihar idan aka kwatanta da abin da ya gada a shekarar 2023.

 

A cewar sa, inganta haɗin gwiwa da jami’an tsaro ya taka muhimmiyar rawa wajen rage yawaitar ayyukan ‘yan bindiga da sauran miyagun ayyuka a Zamfara.

 

Dangane da ababen more rayuwa kuwa, Gwamna Lawal ya ba da misali da ayyukan da ake ci gaba da aiwatarwa da kuma waɗanda aka kammala a ƙarƙashin shirin “Renewal Project,” wanda ya haɗa da gine-gine da gyaran hanyoyi, makarantu, da cibiyoyin kiwon lafiya a dukkanin ƙananan hukumomi goma sha huɗu na jihar.

 

Gwamna Lawal ya kuma bayyana shirin gwamnatin sa na bunƙasa fannin haƙar ma’adanai, inda ya bayyana shi a matsayin wani muhimmin fanni na bunƙasar tattalin arziki da ake samu a yanzu da aka samu daidaiton tsaro a jihar.

 

Da yake jaddada ƙudirin gwamnatin sa na tabbatar da gaskiya da riƙon amana da kuma tafiyar ci gaban al’umma, Gwamna Lawal ya nanata cewa duk nasarorin da aka samu ya zuwa yanzu an cimmasu ne ba tare da karbar rancen ko kobo ɗaya ba.

 

Ya kuma tabbatar wa da al’ummar jihar Zamfara cewa akwai wasu ayyukan ci gaba a nan gaba, domin gwamnatin sa ta ci gaba da mayar da hankali wajen ganin an samar da ci gaba mai ɗorewa da inganta rayuwar al’umma a faɗin jihar.

 

Da ya ke amsa tambaya dangane da rikicin PDP, Gwamna Lawal ya yi imanin cewa rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar PDP ya wuce ɗan takarar ta na shugaban ƙasa a zaben 2023, Atiku Abubakar, kuma ya samo asali ne daga faɗan son rai a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar.

 

“Kowa yana da nasa batun; ba wai batun Atiku Abubakar ba ne, ya wuce shi,” inji shi.

 

“Matsala ce ta cikin gida a cikin PDP, kuma muna yin ƙoƙari sosai. Ina ganin abin ya shafi kishin mutane ne, kowa da kowa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yakin Iran Da Isra’ila Ya Haifar Da Tashin Farashin Litar Man Fetur A Nijeriya

Next Post

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

Related

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi
Labarai

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

2 hours ago
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Labarai

Yakin Iran Da Isra’ila Ya Haifar Da Tashin Farashin Litar Man Fetur A Nijeriya

4 hours ago
Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya
Manyan Labarai

Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

6 hours ago
Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u
Tsaro

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

18 hours ago
Tinubu Ya Yi Allah-Wadai Da Harin Bam A Borno, Ya Yi Alhinin Fashewar Wani A Kano
Labarai

Tinubu Ya Yi Allah-Wadai Da Harin Bam A Borno, Ya Yi Alhinin Fashewar Wani A Kano

20 hours ago
Barayin Wayar Lantarki Sun Addabi A’lummar Jihar Kebbi
Labarai

Barayin Wayar Lantarki Sun Addabi A’lummar Jihar Kebbi

21 hours ago
Next Post
Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami'ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

June 23, 2025
Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

June 23, 2025
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Yakin Iran Da Isra’ila Ya Haifar Da Tashin Farashin Litar Man Fetur A Nijeriya

June 23, 2025
Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

June 23, 2025
Gwamnan Abba Kabir Yusuf tare da Arch. Ali Hassan

Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan

June 23, 2025
2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

June 22, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

June 22, 2025
Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

June 22, 2025
Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

June 22, 2025
Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

June 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.