• English
  • Business News
Saturday, August 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

by Sulaiman
2 months ago
in Labarai
0
Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya bayyana cewa gwamnatinsa ba ta karbi lamuni ko rance domin gudanar da ayyukan kawo sauyi da ake yi a duk faɗin jihar ba, kuma duk da haka yana da isassun kuɗi a ausun jihar.

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne a yayin tattaunawa da ya yi da wasu Editoci a ofishin sa da ke Gusau, babban birnin jihar a ranar Laraba, inda ya yi cikakken bayani kan nasarorin da gwamnatin sa ta samu tun hawan sa mulki kusan shekaru biyu da suka gabata.

  • Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?
  • Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

Gwamna Lawal ya bayyana manyan ci gaban da aka samu a bangarori masu muhimmanci da suka haɗa da tsaro, ilimi, kiwon lafiya, ababen more rayuwa, da ƙarfafa tattalin arziki.

 

Labarai Masu Nasaba

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

Ya nanata cewa nasarar da aka samu ya zuwa yanzu ta samo asali ne sakamakon kyawawan tsare-tsare, ingantaccen jagoranci, da kuma kula da albarkatu.

 

Gwamnan ya bayyana cewa an samu ci gaba sosai a harkar tsaro a jihar idan aka kwatanta da abin da ya gada a shekarar 2023.

 

A cewar sa, inganta haɗin gwiwa da jami’an tsaro ya taka muhimmiyar rawa wajen rage yawaitar ayyukan ‘yan bindiga da sauran miyagun ayyuka a Zamfara.

 

Dangane da ababen more rayuwa kuwa, Gwamna Lawal ya ba da misali da ayyukan da ake ci gaba da aiwatarwa da kuma waɗanda aka kammala a ƙarƙashin shirin “Renewal Project,” wanda ya haɗa da gine-gine da gyaran hanyoyi, makarantu, da cibiyoyin kiwon lafiya a dukkanin ƙananan hukumomi goma sha huɗu na jihar.

 

Gwamna Lawal ya kuma bayyana shirin gwamnatin sa na bunƙasa fannin haƙar ma’adanai, inda ya bayyana shi a matsayin wani muhimmin fanni na bunƙasar tattalin arziki da ake samu a yanzu da aka samu daidaiton tsaro a jihar.

 

Da yake jaddada ƙudirin gwamnatin sa na tabbatar da gaskiya da riƙon amana da kuma tafiyar ci gaban al’umma, Gwamna Lawal ya nanata cewa duk nasarorin da aka samu ya zuwa yanzu an cimmasu ne ba tare da karbar rancen ko kobo ɗaya ba.

 

Ya kuma tabbatar wa da al’ummar jihar Zamfara cewa akwai wasu ayyukan ci gaba a nan gaba, domin gwamnatin sa ta ci gaba da mayar da hankali wajen ganin an samar da ci gaba mai ɗorewa da inganta rayuwar al’umma a faɗin jihar.

 

Da ya ke amsa tambaya dangane da rikicin PDP, Gwamna Lawal ya yi imanin cewa rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar PDP ya wuce ɗan takarar ta na shugaban ƙasa a zaben 2023, Atiku Abubakar, kuma ya samo asali ne daga faɗan son rai a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar.

 

“Kowa yana da nasa batun; ba wai batun Atiku Abubakar ba ne, ya wuce shi,” inji shi.

 

“Matsala ce ta cikin gida a cikin PDP, kuma muna yin ƙoƙari sosai. Ina ganin abin ya shafi kishin mutane ne, kowa da kowa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yakin Iran Da Isra’ila Ya Haifar Da Tashin Farashin Litar Man Fetur A Nijeriya

Next Post

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

Related

Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

5 hours ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

6 hours ago
Legas Ta Laƙume Aikin Naira Tiriliyan 3.9 Cikin Shekaru Biyun Tinubu
Manyan Labarai

Legas Ta Laƙume Aikin Naira Tiriliyan 3.9 Cikin Shekaru Biyun Tinubu

7 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Ceto Wani Dan Shekara 25 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

9 hours ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Tsaro

An Cafke Mutum Hudu Bayan ‘Yan Fashi 20 Sun Afka Wasu Gidaje A Bauchi

10 hours ago
NDLEA Ta Kama Wani Matashi Dan Shekara 29 Da Kwayoyin Tramadol 7,000 A Kano
Tsaro

NDLEA Ta Kama Wani Matashi Dan Shekara 29 Da Kwayoyin Tramadol 7,000 A Kano

11 hours ago
Next Post
Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami'ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

LABARAI MASU NASABA

Gyaran fuska

Gyaran Fuska Da Laushin Fata

August 30, 2025
Shugaban Belarus Ya Jinjinawa Gudummawar Sin A Fannin Inganta Ci Gaban Kungiyar SCO

Shugaban Belarus Ya Jinjinawa Gudummawar Sin A Fannin Inganta Ci Gaban Kungiyar SCO

August 30, 2025
majalisar kasa

Tarihin ‘Yan Majalisar Farko A Nijeriya Kafin Zamanin Mulkin Mallaka

August 30, 2025
Sin Da AU Sun Sabunta Hadin Gwiwa Game Da Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani Wajen Raya Noma A Afirka

Sin Da AU Sun Sabunta Hadin Gwiwa Game Da Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani Wajen Raya Noma A Afirka

August 30, 2025
Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa

Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa

August 30, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Musayar Ra’ayoyi Game Da Batutuwan Cinikayya

Sin Da Amurka Sun Yi Musayar Ra’ayoyi Game Da Batutuwan Cinikayya

August 30, 2025
Lambar Yabo Ta CON: Buni Ya Zama Zinare Bashi Da Maboya

NTIC Ta Jinjina Wa Gwamna Buni Kan Taimako A Bangaren Ilimi

August 30, 2025
Ra’ayoyin Jama’a Daga Kuri’ar CGTN Sun Jinjinawa Gudummawar Sin A Fannin Raya Kungiyar SCO

Ra’ayoyin Jama’a Daga Kuri’ar CGTN Sun Jinjinawa Gudummawar Sin A Fannin Raya Kungiyar SCO

August 30, 2025
Rasmus Højlund Ya Sauya Sheƙa Zuwa Napoli A Matsayin Aro Daga Manchester United

Rasmus Højlund Ya Sauya Sheƙa Zuwa Napoli A Matsayin Aro Daga Manchester United

August 30, 2025
Hukumar SUBEB Ta Yi Kira Ga Al’umma Da Su Sa ‘Ya’yansu Makaranta

Hukumar SUBEB Ta Yi Kira Ga Al’umma Da Su Sa ‘Ya’yansu Makaranta

August 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.