• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

by Yusuf Shuaibu
4 months ago
INEC

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta tsaida ranar 16 ga Agusta don gudanar da zabe cike gibi a mazabe 16 da ke a jihohi 12 na tarayyar Nijeriya.

Hukumar ta kara da cewa za ta tura jami’ai 30,451 don gudanar da zaben, kuma ta sanar da ci gaba da yin rajistar zabe a duk fadin kasar, daga ranar 18 ga watan Agusta.

  • Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya
  • Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota

Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, wanda ya bayyana wannan a taron tattaunawa tare da jam’iyyar siyasa a Abuja, ya ce bisa ga korafe-korafen da ke fitowa daga jam’iyyun adawa na cewa wadanda suka dade suna rike da mukamai sukan hana su samun damar amfani da wuraren gwamnatin, ciki har da kafofin watsa labarai na gwamnati.

Ya ce daga yanzu, hukumar za ta yi aiki tare cibiyar hadakar jam’iyyu (IPAC) da hukumar kula da tallace-tallace ta Nijeriya (ARCON), don daukar matakin shari’a kan masu irin wannan laifi.

Yakubu ya ce, “Yayin da ake fara ayyukan yakin neman zabe a Jihar Anambra, ina so in jawo hankali ga masu korafe-korafe musamman jam’iyyun adawa game da Rashin bayar da damar shiga wuraren gwamnati don gudanar da ayyukan zabe. Wadannan sun hada da kafofin yada labarai na jihar, gine-ginen gwamnati don taruka da kuma wuraren da ake kibe don yin gangamin da taruka.”

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

“A wasu lokutan, ana cajin kudi masu yawa waje tallace-tallace. Wadannan abubuwan na cikin rashin bin doka a cikin dokar zabe ta 2022 wadda ke hana amfani da matsayi don musguna wa kowanne jam’iyya ko dan takara.

“Hukumarmu za ta yi aiki tare da cibiyar hadakar jam’iyyu (IPAC), kuma za mu kara karfafa hadin gwiwarmu da hukumar kula da tallace-tallace ta Nijeriya (ARCON), don daukar matakin doka idan aka samu shaidu masu karfi na karya doka.

“Game da zaben cike gibi kuwa, bari in ba ku takaitaccen bayani kan lamarin. A cikin shekaru biyu da suka gabata tun lokacin kaddamar da majalisun kasa da na jihohi a watan Yunin 2023, an samu kujerun ‘yan majalisa da babu kowa wanda ake bukatar yi zabe a fadin kasar nan.

“Idan za ku iya tunawa cewa a watan Fabrairu na shekarar da ta gabata, hukumar ta gudanar da zaben cike gurbi domin cike kujeru guda tara da aka samu sakamakon mutuwar ko murabus na ‘yan majalisun tarayya na jihohi. Tun daga wannan lokacin, an samu karin gurabe a fadin kasar nan.

“A saboda haka, hukumar ta fitar da ranar Asabar, 16 ga Agusta, 2025, don gudanar da zaben cike gibi a mazabu 16 a da ke jihohi 12 na kasar nan, wanda ya kunshin adadin masu zabe 3,553,659 da aka yi wa rajista, wanda aka rarraba a cikin kananan hukumomi 32, wuraren zabe 356 da kuma rukunin zaben 6,987. Hukumar za ta tura jami’ai 30,451,” in ji shugaban INCE.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

October 24, 2025
Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

October 24, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.