ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

by Yusuf Shuaibu
12 months ago
INEC

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta tsaida ranar 16 ga Agusta don gudanar da zabe cike gibi a mazabe 16 da ke a jihohi 12 na tarayyar Nijeriya.

Hukumar ta kara da cewa za ta tura jami’ai 30,451 don gudanar da zaben, kuma ta sanar da ci gaba da yin rajistar zabe a duk fadin kasar, daga ranar 18 ga watan Agusta.

  • Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya
  • Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota

Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, wanda ya bayyana wannan a taron tattaunawa tare da jam’iyyar siyasa a Abuja, ya ce bisa ga korafe-korafen da ke fitowa daga jam’iyyun adawa na cewa wadanda suka dade suna rike da mukamai sukan hana su samun damar amfani da wuraren gwamnatin, ciki har da kafofin watsa labarai na gwamnati.

ADVERTISEMENT

Ya ce daga yanzu, hukumar za ta yi aiki tare cibiyar hadakar jam’iyyu (IPAC) da hukumar kula da tallace-tallace ta Nijeriya (ARCON), don daukar matakin shari’a kan masu irin wannan laifi.

Yakubu ya ce, “Yayin da ake fara ayyukan yakin neman zabe a Jihar Anambra, ina so in jawo hankali ga masu korafe-korafe musamman jam’iyyun adawa game da Rashin bayar da damar shiga wuraren gwamnati don gudanar da ayyukan zabe. Wadannan sun hada da kafofin yada labarai na jihar, gine-ginen gwamnati don taruka da kuma wuraren da ake kibe don yin gangamin da taruka.”

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

“A wasu lokutan, ana cajin kudi masu yawa waje tallace-tallace. Wadannan abubuwan na cikin rashin bin doka a cikin dokar zabe ta 2022 wadda ke hana amfani da matsayi don musguna wa kowanne jam’iyya ko dan takara.

“Hukumarmu za ta yi aiki tare da cibiyar hadakar jam’iyyu (IPAC), kuma za mu kara karfafa hadin gwiwarmu da hukumar kula da tallace-tallace ta Nijeriya (ARCON), don daukar matakin doka idan aka samu shaidu masu karfi na karya doka.

“Game da zaben cike gibi kuwa, bari in ba ku takaitaccen bayani kan lamarin. A cikin shekaru biyu da suka gabata tun lokacin kaddamar da majalisun kasa da na jihohi a watan Yunin 2023, an samu kujerun ‘yan majalisa da babu kowa wanda ake bukatar yi zabe a fadin kasar nan.

“Idan za ku iya tunawa cewa a watan Fabrairu na shekarar da ta gabata, hukumar ta gudanar da zaben cike gurbi domin cike kujeru guda tara da aka samu sakamakon mutuwar ko murabus na ‘yan majalisun tarayya na jihohi. Tun daga wannan lokacin, an samu karin gurabe a fadin kasar nan.

“A saboda haka, hukumar ta fitar da ranar Asabar, 16 ga Agusta, 2025, don gudanar da zaben cike gibi a mazabu 16 a da ke jihohi 12 na kasar nan, wanda ya kunshin adadin masu zabe 3,553,659 da aka yi wa rajista, wanda aka rarraba a cikin kananan hukumomi 32, wuraren zabe 356 da kuma rukunin zaben 6,987. Hukumar za ta tura jami’ai 30,451,” in ji shugaban INCE.

INEC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

June 20, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

June 20, 2026
Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

June 20, 2026
2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.