• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Bukaci A Samar Da Tsaro A Yankunan Zaben Cike Gurbi

byYusuf Shuaibu
2 years ago
INEC

Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) Farfesa Mahmood Yakubu ya bukaci a samar da tsaro a dukkanin yankunan da za gudanar da zaben cike gurbi a kasar nan.

Yakubu ya yi wannan kiran ne a lokacin wata ganawa da kwamitin samar da tsaro kan zabe a Abuja.

  • Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya
  • Gwamatin Tarayya Ta Fito Da Tsarin Cin Gajiyar Ma’adanan da Ke Jihar Nasarawa

Ya bayyana cewa akwai zaben da za a yi a watan Fabrairu har kashi biyu, na farko shi ne, zaben cike gurbi wanda aka samu sakamakon mutuwa ko ajiye aiki ga ‘yan majalisun tarayya da na jiha, inda a zaben zai guda a mazabar ‘yan majalisar dattawa guda biyu da kuma ‘yan majalisar wakilai a jihohi uku. Sannan ya ce zaben kashi na biyu kuma za a gudanar da shi ne sakamakon hukuncin kotu.

Idan za a iya tunawa an gudanar da ire-iren wannan ganawa da shugabannin jam’iyyun siyasa a watan da ya gabata, shugaban INEC ya ce a baya an shirya za a gudanar da zaben cike gibi ne a mazabu 35 da ke fadin kasar nan.

Sai dai ya ce a yanzu haka an samu karin mazabu hudu wanda kotun daukaka kara ta umurci hukumar ta gudanar da zabe a mazabar Yabe/Shagari da ke Jihar Sakwato da Madara/Chiade a Jihar Bauchi da kuma Kudan da Kauru/Chawai na Jihar Kaduna.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

“Da wannan ne aka samu jimillar mazabu 39 za a gudanar da zaben cike gibi a fadin kasar nan baki daya. Daga cikin adadin, mazabu 9 za a gudanar da sabon zabe ne.

“In ban da guda uku daga cikin mazabun da suka hada da Filato ta Arewa da Arewacin Jos/Bassa a Jihar Filato da Kachia/Kagarko a Jihar Kaduna, duk sauran zaben zai gudana ne a akwatunan zabe kalilan. A wasu wuraren kuma, akwatin zabe guda daya ne kawai za a gudanar da zaben.

“Babban aikin kwamitin samar da tsaro shi ne, tabbatar da an gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali da lumana. Bisa wannan dalilin ne, hukunar ta riga ta sanar da cewa rundunar ‘yansandar Nijeriya ce za ta jagoranci al’amuran tsaro a lokacin zabe a dukkanin mazabu da ke fadin kasar nan.

“Mun fitar da adadin yawan masu kada kuri’a da suka amshi katin zabe a dukkanin rumfunan zabe da ke fadin kasar nan.

“Duka bayanan da muka yi a baya su ne muka sake maimaitawa a wannan ganawa da mambobin kwamitin samar da tsaro. Sannan za mu saka dukkan bayanan a shafukan sada zumanta na hukumarmu bayan wannan ganawa saboda fadakar da mutane.

“A matsayinmu na hukumomin tsaro, hakkinku ne ku tsare yankunan da za a gudanar da zaben domin ba mu damar jibge jami’anmu da kayayyakin zabe da tsare masu saka ido ciki har ma da ‘yan jarida da wakilan jam’iyyu da kuma ‘yan takara. Idan har ba a samu tsaro ba a mazabun, ba za mu iya gudanar da sahihin zabe ba.

“Bisa abubuwan da suka gabata a baya, zaben cike gurbi yana da matsaloli masu tarin yawa. Za mu mayar da hankali wajen rage lamarin a bangaren wasu ‘yan takara da kuma magoya bayansu.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Makamashin Lantarki: Kwararru Sun Yi Tawaye Ga Karin Kudin Wuta

Makamashin Lantarki: Kwararru Sun Yi Tawaye Ga Karin Kudin Wuta

LABARAI MASU NASABA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version