ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Bukaci A Samar Da Tsaro A Yankunan Zaben Cike Gurbi

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
INEC

Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) Farfesa Mahmood Yakubu ya bukaci a samar da tsaro a dukkanin yankunan da za gudanar da zaben cike gurbi a kasar nan.

Yakubu ya yi wannan kiran ne a lokacin wata ganawa da kwamitin samar da tsaro kan zabe a Abuja.

  • Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya
  • Gwamatin Tarayya Ta Fito Da Tsarin Cin Gajiyar Ma’adanan da Ke Jihar Nasarawa

Ya bayyana cewa akwai zaben da za a yi a watan Fabrairu har kashi biyu, na farko shi ne, zaben cike gurbi wanda aka samu sakamakon mutuwa ko ajiye aiki ga ‘yan majalisun tarayya da na jiha, inda a zaben zai guda a mazabar ‘yan majalisar dattawa guda biyu da kuma ‘yan majalisar wakilai a jihohi uku. Sannan ya ce zaben kashi na biyu kuma za a gudanar da shi ne sakamakon hukuncin kotu.

ADVERTISEMENT

Idan za a iya tunawa an gudanar da ire-iren wannan ganawa da shugabannin jam’iyyun siyasa a watan da ya gabata, shugaban INEC ya ce a baya an shirya za a gudanar da zaben cike gibi ne a mazabu 35 da ke fadin kasar nan.

Sai dai ya ce a yanzu haka an samu karin mazabu hudu wanda kotun daukaka kara ta umurci hukumar ta gudanar da zabe a mazabar Yabe/Shagari da ke Jihar Sakwato da Madara/Chiade a Jihar Bauchi da kuma Kudan da Kauru/Chawai na Jihar Kaduna.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

“Da wannan ne aka samu jimillar mazabu 39 za a gudanar da zaben cike gibi a fadin kasar nan baki daya. Daga cikin adadin, mazabu 9 za a gudanar da sabon zabe ne.

“In ban da guda uku daga cikin mazabun da suka hada da Filato ta Arewa da Arewacin Jos/Bassa a Jihar Filato da Kachia/Kagarko a Jihar Kaduna, duk sauran zaben zai gudana ne a akwatunan zabe kalilan. A wasu wuraren kuma, akwatin zabe guda daya ne kawai za a gudanar da zaben.

“Babban aikin kwamitin samar da tsaro shi ne, tabbatar da an gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali da lumana. Bisa wannan dalilin ne, hukunar ta riga ta sanar da cewa rundunar ‘yansandar Nijeriya ce za ta jagoranci al’amuran tsaro a lokacin zabe a dukkanin mazabu da ke fadin kasar nan.

“Mun fitar da adadin yawan masu kada kuri’a da suka amshi katin zabe a dukkanin rumfunan zabe da ke fadin kasar nan.

“Duka bayanan da muka yi a baya su ne muka sake maimaitawa a wannan ganawa da mambobin kwamitin samar da tsaro. Sannan za mu saka dukkan bayanan a shafukan sada zumanta na hukumarmu bayan wannan ganawa saboda fadakar da mutane.

“A matsayinmu na hukumomin tsaro, hakkinku ne ku tsare yankunan da za a gudanar da zaben domin ba mu damar jibge jami’anmu da kayayyakin zabe da tsare masu saka ido ciki har ma da ‘yan jarida da wakilan jam’iyyu da kuma ‘yan takara. Idan har ba a samu tsaro ba a mazabun, ba za mu iya gudanar da sahihin zabe ba.

“Bisa abubuwan da suka gabata a baya, zaben cike gurbi yana da matsaloli masu tarin yawa. Za mu mayar da hankali wajen rage lamarin a bangaren wasu ‘yan takara da kuma magoya bayansu.”

INEC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Makamashin Lantarki: Kwararru Sun Yi Tawaye Ga Karin Kudin Wuta

Makamashin Lantarki: Kwararru Sun Yi Tawaye Ga Karin Kudin Wuta

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.