ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Bukaci A Samar Da Tsaro A Yankunan Zaben Cike Gurbi

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
INEC

Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) Farfesa Mahmood Yakubu ya bukaci a samar da tsaro a dukkanin yankunan da za gudanar da zaben cike gurbi a kasar nan.

Yakubu ya yi wannan kiran ne a lokacin wata ganawa da kwamitin samar da tsaro kan zabe a Abuja.

  • Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya
  • Gwamatin Tarayya Ta Fito Da Tsarin Cin Gajiyar Ma’adanan da Ke Jihar Nasarawa

Ya bayyana cewa akwai zaben da za a yi a watan Fabrairu har kashi biyu, na farko shi ne, zaben cike gurbi wanda aka samu sakamakon mutuwa ko ajiye aiki ga ‘yan majalisun tarayya da na jiha, inda a zaben zai guda a mazabar ‘yan majalisar dattawa guda biyu da kuma ‘yan majalisar wakilai a jihohi uku. Sannan ya ce zaben kashi na biyu kuma za a gudanar da shi ne sakamakon hukuncin kotu.

ADVERTISEMENT

Idan za a iya tunawa an gudanar da ire-iren wannan ganawa da shugabannin jam’iyyun siyasa a watan da ya gabata, shugaban INEC ya ce a baya an shirya za a gudanar da zaben cike gibi ne a mazabu 35 da ke fadin kasar nan.

Sai dai ya ce a yanzu haka an samu karin mazabu hudu wanda kotun daukaka kara ta umurci hukumar ta gudanar da zabe a mazabar Yabe/Shagari da ke Jihar Sakwato da Madara/Chiade a Jihar Bauchi da kuma Kudan da Kauru/Chawai na Jihar Kaduna.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

“Da wannan ne aka samu jimillar mazabu 39 za a gudanar da zaben cike gibi a fadin kasar nan baki daya. Daga cikin adadin, mazabu 9 za a gudanar da sabon zabe ne.

“In ban da guda uku daga cikin mazabun da suka hada da Filato ta Arewa da Arewacin Jos/Bassa a Jihar Filato da Kachia/Kagarko a Jihar Kaduna, duk sauran zaben zai gudana ne a akwatunan zabe kalilan. A wasu wuraren kuma, akwatin zabe guda daya ne kawai za a gudanar da zaben.

“Babban aikin kwamitin samar da tsaro shi ne, tabbatar da an gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali da lumana. Bisa wannan dalilin ne, hukunar ta riga ta sanar da cewa rundunar ‘yansandar Nijeriya ce za ta jagoranci al’amuran tsaro a lokacin zabe a dukkanin mazabu da ke fadin kasar nan.

“Mun fitar da adadin yawan masu kada kuri’a da suka amshi katin zabe a dukkanin rumfunan zabe da ke fadin kasar nan.

“Duka bayanan da muka yi a baya su ne muka sake maimaitawa a wannan ganawa da mambobin kwamitin samar da tsaro. Sannan za mu saka dukkan bayanan a shafukan sada zumanta na hukumarmu bayan wannan ganawa saboda fadakar da mutane.

“A matsayinmu na hukumomin tsaro, hakkinku ne ku tsare yankunan da za a gudanar da zaben domin ba mu damar jibge jami’anmu da kayayyakin zabe da tsare masu saka ido ciki har ma da ‘yan jarida da wakilan jam’iyyu da kuma ‘yan takara. Idan har ba a samu tsaro ba a mazabun, ba za mu iya gudanar da sahihin zabe ba.

“Bisa abubuwan da suka gabata a baya, zaben cike gurbi yana da matsaloli masu tarin yawa. Za mu mayar da hankali wajen rage lamarin a bangaren wasu ‘yan takara da kuma magoya bayansu.”

INEC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Makamashin Lantarki: Kwararru Sun Yi Tawaye Ga Karin Kudin Wuta

Makamashin Lantarki: Kwararru Sun Yi Tawaye Ga Karin Kudin Wuta

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.