• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Makamashin Lantarki: Kwararru Sun Yi Tawaye Ga Karin Kudin Wuta

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Kimiyya Da Fasahar Sadarwa
0
Makamashin Lantarki: Kwararru Sun Yi Tawaye Ga Karin Kudin Wuta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwararru a harka sha’anin wutar lantarki sun yi bore ga umarnin karin kudin wutar lantarki na shekara-shekara (MYTO) da hukumar kula da harkokin wutar lantarki ta kasa (NERC) ta yi, inda lamarin ke ci gaba da janyo muhawara da tayar da kura a tsakanin masu ruwa da tsaki a harka wutar lantarki.

Sabon umarnin na NERCs da ya bai wa kamfanonin rarraba wutar lantarki su 11 damar kara kudin wuta, zai ninka kudin wutar lantarki kan yadda kwastomomi suke biya a baya, a shekarar 2024.

  • Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya
  • Gwamatin Tarayya Ta Fito Da Tsarin Cin Gajiyar Ma’adanan da Ke Jihar Nasarawa

 A yayin da gwamnati kuma ta dauki nauyin biyan Naira tiriliyan 1.6, kasafin kudin kamfanin lantarki na Nijeriya na shekarar 2024 ya nuna cewa akwai tsarin biyan tallafin naira biliyan 450, lamarin da ke nuni da cewa gwamnati za ta nemo kudi a ciki ko kasuwannin waje.

Masani a bangaren makamashin sun yi gargadin cewa, kara kudin lantarki kai tsaye na nuni ne da cewa za a samu karin farashin abubuwa da karin kudaden kasuwanci, rasa ayyukan yi, hauhawar farashin kayan masarufi da uwa uba kara jefa al’ummar kasa musamman talakawa cikin matsanatsi da kuncin rayuwa.

Wannan karin na zuwa ne yayin da bayanai ke nuni da cewa adadin kwastomomi 51,631 ke amfani da mitar kamfanonin rarraba wutar lantarki guda 11 ya zuwa watan Nuwamban 2023.

Labarai Masu Nasaba

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

Yayin da kuma masu amfani da wuta da basu amfani da mitoci suka kai 7,313,039 a cewar NERC.

A cewar hukumar jimillar wadanda suka yi rijista da NESI zuwa Nuwamba, 2023 sun kai 13,112,134, yayin da kuma jimillar kwastomomin da ke da mitoci su 5,799,095, inda adadin amfani da mitocin ya kai kaso 44.23 cikin 100.

Da ya ke tofa albarkacin bakinsa kan karin kudin, shugaban kwastamomi na kungiyar NCPN, Kunle Kola Olubiyo, ya yi gargadin cewa karin kudin lantarki zai kai ga janyo hauhawar rashin kayan masarufi da tsadar gudanar da lamura hadi da jefa jama’an kasa cikin kunci mai muni.

Olubiyo ya nace kan cewa mutane da dama sun dogara da wutar lantarki domin neman na kaiwa bakin salati.

Shi kuma a nasa bangaren, manajan gudanarwa na Mainstream Energy Solutions, Audu Lamu, ya ce, zuba tallafin kudin lantarki ba hanyace da ke daurewa ba, kuma hakan na jefa wa masu zuba hannun jari shakkun yin hulda.

A cewarsa, tallafi ba zai bai wa masu zuba hannun jari kwarin guiwa ba, saboda hakan ba zai shawo kan dukkanin matsalolin da harkar ke fuskanta ba.

Shi ma kwararre a bangaren makamashi daga jami’ar Ibadan, Farfesa Adeola Adenikinju, ya ce, tallafi ba zai iya shawo kan matsalolin da suke akwai a bangaren lantarki ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

INEC Ta Bukaci A Samar Da Tsaro A Yankunan Zaben Cike Gurbi

Next Post

Ƙungiyar Masu Sana’ar POS Za Ta Fara Aikin Taftace Sana’ar A Faɗin Kasar Nan

Related

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

3 months ago
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

4 months ago
Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet

5 months ago
Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet

5 months ago
Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani

10 months ago
Yadda Na Kirkiro ‘Brain-chip’ Da Ke Dawo Wa Wadanda Aka Haifa Da Makanta Ganinsu – Elon Musk
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Na Kirkiro ‘Brain-chip’ Da Ke Dawo Wa Wadanda Aka Haifa Da Makanta Ganinsu – Elon Musk

10 months ago
Next Post
Ƙungiyar Masu Sana’ar POS Za Ta Fara Aikin Taftace Sana’ar A Faɗin Kasar Nan

Ƙungiyar Masu Sana’ar POS Za Ta Fara Aikin Taftace Sana’ar A Faɗin Kasar Nan

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.