ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Makamashin Lantarki: Kwararru Sun Yi Tawaye Ga Karin Kudin Wuta

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Lantarki

Kwararru a harka sha’anin wutar lantarki sun yi bore ga umarnin karin kudin wutar lantarki na shekara-shekara (MYTO) da hukumar kula da harkokin wutar lantarki ta kasa (NERC) ta yi, inda lamarin ke ci gaba da janyo muhawara da tayar da kura a tsakanin masu ruwa da tsaki a harka wutar lantarki.

Sabon umarnin na NERCs da ya bai wa kamfanonin rarraba wutar lantarki su 11 damar kara kudin wuta, zai ninka kudin wutar lantarki kan yadda kwastomomi suke biya a baya, a shekarar 2024.

  • Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya
  • Gwamatin Tarayya Ta Fito Da Tsarin Cin Gajiyar Ma’adanan da Ke Jihar Nasarawa

 A yayin da gwamnati kuma ta dauki nauyin biyan Naira tiriliyan 1.6, kasafin kudin kamfanin lantarki na Nijeriya na shekarar 2024 ya nuna cewa akwai tsarin biyan tallafin naira biliyan 450, lamarin da ke nuni da cewa gwamnati za ta nemo kudi a ciki ko kasuwannin waje.

ADVERTISEMENT

Masani a bangaren makamashin sun yi gargadin cewa, kara kudin lantarki kai tsaye na nuni ne da cewa za a samu karin farashin abubuwa da karin kudaden kasuwanci, rasa ayyukan yi, hauhawar farashin kayan masarufi da uwa uba kara jefa al’ummar kasa musamman talakawa cikin matsanatsi da kuncin rayuwa.

Wannan karin na zuwa ne yayin da bayanai ke nuni da cewa adadin kwastomomi 51,631 ke amfani da mitar kamfanonin rarraba wutar lantarki guda 11 ya zuwa watan Nuwamban 2023.

LABARAI MASU NASABA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Yayin da kuma masu amfani da wuta da basu amfani da mitoci suka kai 7,313,039 a cewar NERC.

A cewar hukumar jimillar wadanda suka yi rijista da NESI zuwa Nuwamba, 2023 sun kai 13,112,134, yayin da kuma jimillar kwastomomin da ke da mitoci su 5,799,095, inda adadin amfani da mitocin ya kai kaso 44.23 cikin 100.

Da ya ke tofa albarkacin bakinsa kan karin kudin, shugaban kwastamomi na kungiyar NCPN, Kunle Kola Olubiyo, ya yi gargadin cewa karin kudin lantarki zai kai ga janyo hauhawar rashin kayan masarufi da tsadar gudanar da lamura hadi da jefa jama’an kasa cikin kunci mai muni.

Olubiyo ya nace kan cewa mutane da dama sun dogara da wutar lantarki domin neman na kaiwa bakin salati.

Shi kuma a nasa bangaren, manajan gudanarwa na Mainstream Energy Solutions, Audu Lamu, ya ce, zuba tallafin kudin lantarki ba hanyace da ke daurewa ba, kuma hakan na jefa wa masu zuba hannun jari shakkun yin hulda.

A cewarsa, tallafi ba zai bai wa masu zuba hannun jari kwarin guiwa ba, saboda hakan ba zai shawo kan dukkanin matsalolin da harkar ke fuskanta ba.

Shi ma kwararre a bangaren makamashi daga jami’ar Ibadan, Farfesa Adeola Adenikinju, ya ce, tallafi ba zai iya shawo kan matsalolin da suke akwai a bangaren lantarki ba.

Lantarki
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

February 21, 2026
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

April 19, 2025
Next Post
Ƙungiyar Masu Sana’ar POS Za Ta Fara Aikin Taftace Sana’ar A Faɗin Kasar Nan

Ƙungiyar Masu Sana’ar POS Za Ta Fara Aikin Taftace Sana’ar A Faɗin Kasar Nan

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.