• English
  • Business News
Friday, August 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Goge Sunayen Matattu 7,746 Daga Rajistar Zabe

by Yusuf Shuaibu
7 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
‘Yansanda Sun Kama Wani Mutum Da Katin Zabe Sama Da 100 A Sakkwato 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta sanar da cewa an cire sunayen matattun masu kada kuri’a har guda 7,746 daga rajistar masu zabe a jihohi 36 da kuma Babban Birnin Tarayya Abuja a zuwa watan Disambar 2022.

Daraktar wayar da kan jama’a da masu kada kuri’a, Bictoria Etta-Messi ce ta bayyana hakan ga manema labarai.

  • A Shirye Kasar Sin Take Ta Kyautata Dangantakar Tattalin Arziki Da Amurka
  • Shirin Tallafinmu Ga Nijeriya A 2025 Zai Kai Ga Asalin Mabukata – Wakilin MDD

“Mutane dubu bakwai da dari bakwai da arba’in da shida sun ragu a fadin jihohi 36 da kuma Babban Birnin Tarayya Abuja daga rajistar masu kada kuri’a zuwa watan Disamba 2022,” in ji ta.

A cewar hukumar INEC, ana tsaftace rajistar masu kada kuri’a kafin kowane babban zabe.

A bitar zaben 2023 bayan kammala zabe a watan Disamba na 2024, INEC ta bayyana kalubalen da ke tattare da tsaftace rajistar masu kada kuri’a, duk da ingantuwar tsarin rajistar masu kada kuri’a da aka samu wanda ya kara sabbin masu rajista har guda 12,298,944.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Wani babban batu shi ne, wahalar cire wadanda suka mutu sakamakon gibin bayanan mutuwar a hukumance.

“Matsalolin da ke tattare da bayanan mutuwar jami’ai na ci gaba da yin wahala ga INEC wajen cire wadanda suka mutu rajistar zabe,” in ji hukumar.

Hukumar ta kuma gano matsalar yin rajista sau biyu ko kuma da yawa, wanda aka magance ta hanyar tura na’urar tantance bayanan masu kada kuri’a.

Wannan tsari ya ba da alama tare da cire shari’o’in 2,780,756 na rajista marasa inganci, wanda ke wakiltar kashi 22.6 na duk sabbin masu rajista a fadin kasar nan.

INEC ta kara nuna damuwa game da raguwar fitowar masu kada kuri’a. Zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar dokokin kasar a shekarar 2023, ya samu fitowar kashi 27.5 cikin 100, inda ya ragu da kashi 35.6 a shekarar 2019.

Wasu masu ruwa da tsaki sun alakanta wannan raguwar wani bangare na hauhawar rajistar masu kada kuri’a tare da yin kira da a kara himma wajen tsaftace ta.

Masu ruwa da tsaki a wannan bitar sun ba da shawarar cewa ya kamata INEC ta karfafa hadin gwiwa da hukumomi irinsu hukumar kula da yawan jama’a ta kasa (NPC) da kuma hukumar kula da tantance ‘yan kasa (NIMC) domin tantance wadanda suka mutu.

Akwai kuma kiraye-kirayen a dakatar da mutanen da ba su yi zabe ba a zabuka uku da suka gabata da kuma bukatar su sake sabunta rajistarsu.

“Shawara daya daga cikin wannan bita ita ce a karfafa hadin gwiwa da sauran hukumomi irinsu NIMC da NPC don zakulo wadanda suka rasu a cikin rajista da cire su. Bugu da kari, hukumar za ta iya dakatar da mutanen da ba su yi zabe ba a zabuka uku da suka gabata daga rajistar tare da neman su sabunta rajistarsu,” in ji INEC a bitarta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: INECKatin Zabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yara 536,000 Ba Sa Zuwa Makaranta A Katsina – UNICEF

Next Post

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda, Sun Kama Masu Safarar Makamai, Sun Ceto Mutane

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

2 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

2 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

3 weeks ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

3 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

4 weeks ago
Next Post
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda, Sun Kama Masu Safarar Makamai, Sun Ceto Mutane

LABARAI MASU NASABA

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

August 8, 2025
Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

August 8, 2025
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

August 8, 2025
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

August 8, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

August 8, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro

August 8, 2025
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

August 8, 2025
Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

August 8, 2025
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

August 8, 2025
Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 

Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.