• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Goge Sunayen Matattu 7,746 Daga Rajistar Zabe

by Yusuf Shuaibu
6 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
‘Yansanda Sun Kama Wani Mutum Da Katin Zabe Sama Da 100 A Sakkwato 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta sanar da cewa an cire sunayen matattun masu kada kuri’a har guda 7,746 daga rajistar masu zabe a jihohi 36 da kuma Babban Birnin Tarayya Abuja a zuwa watan Disambar 2022.

Daraktar wayar da kan jama’a da masu kada kuri’a, Bictoria Etta-Messi ce ta bayyana hakan ga manema labarai.

  • A Shirye Kasar Sin Take Ta Kyautata Dangantakar Tattalin Arziki Da Amurka
  • Shirin Tallafinmu Ga Nijeriya A 2025 Zai Kai Ga Asalin Mabukata – Wakilin MDD

“Mutane dubu bakwai da dari bakwai da arba’in da shida sun ragu a fadin jihohi 36 da kuma Babban Birnin Tarayya Abuja daga rajistar masu kada kuri’a zuwa watan Disamba 2022,” in ji ta.

A cewar hukumar INEC, ana tsaftace rajistar masu kada kuri’a kafin kowane babban zabe.

A bitar zaben 2023 bayan kammala zabe a watan Disamba na 2024, INEC ta bayyana kalubalen da ke tattare da tsaftace rajistar masu kada kuri’a, duk da ingantuwar tsarin rajistar masu kada kuri’a da aka samu wanda ya kara sabbin masu rajista har guda 12,298,944.

Labarai Masu Nasaba

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

Wani babban batu shi ne, wahalar cire wadanda suka mutu sakamakon gibin bayanan mutuwar a hukumance.

“Matsalolin da ke tattare da bayanan mutuwar jami’ai na ci gaba da yin wahala ga INEC wajen cire wadanda suka mutu rajistar zabe,” in ji hukumar.

Hukumar ta kuma gano matsalar yin rajista sau biyu ko kuma da yawa, wanda aka magance ta hanyar tura na’urar tantance bayanan masu kada kuri’a.

Wannan tsari ya ba da alama tare da cire shari’o’in 2,780,756 na rajista marasa inganci, wanda ke wakiltar kashi 22.6 na duk sabbin masu rajista a fadin kasar nan.

INEC ta kara nuna damuwa game da raguwar fitowar masu kada kuri’a. Zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar dokokin kasar a shekarar 2023, ya samu fitowar kashi 27.5 cikin 100, inda ya ragu da kashi 35.6 a shekarar 2019.

Wasu masu ruwa da tsaki sun alakanta wannan raguwar wani bangare na hauhawar rajistar masu kada kuri’a tare da yin kira da a kara himma wajen tsaftace ta.

Masu ruwa da tsaki a wannan bitar sun ba da shawarar cewa ya kamata INEC ta karfafa hadin gwiwa da hukumomi irinsu hukumar kula da yawan jama’a ta kasa (NPC) da kuma hukumar kula da tantance ‘yan kasa (NIMC) domin tantance wadanda suka mutu.

Akwai kuma kiraye-kirayen a dakatar da mutanen da ba su yi zabe ba a zabuka uku da suka gabata da kuma bukatar su sake sabunta rajistarsu.

“Shawara daya daga cikin wannan bita ita ce a karfafa hadin gwiwa da sauran hukumomi irinsu NIMC da NPC don zakulo wadanda suka rasu a cikin rajista da cire su. Bugu da kari, hukumar za ta iya dakatar da mutanen da ba su yi zabe ba a zabuka uku da suka gabata daga rajistar tare da neman su sabunta rajistarsu,” in ji INEC a bitarta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: INECKatin Zabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yara 536,000 Ba Sa Zuwa Makaranta A Katsina – UNICEF

Next Post

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda, Sun Kama Masu Safarar Makamai, Sun Ceto Mutane

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

3 hours ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

4 hours ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

5 days ago
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Tambarin Dimokuradiyya

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

7 days ago
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

1 week ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

1 week ago
Next Post
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda, Sun Kama Masu Safarar Makamai, Sun Ceto Mutane

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.