ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Goge Sunayen Matattu 7,746 Daga Rajistar Zabe

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
INEC

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta sanar da cewa an cire sunayen matattun masu kada kuri’a har guda 7,746 daga rajistar masu zabe a jihohi 36 da kuma Babban Birnin Tarayya Abuja a zuwa watan Disambar 2022.

Daraktar wayar da kan jama’a da masu kada kuri’a, Bictoria Etta-Messi ce ta bayyana hakan ga manema labarai.

  • A Shirye Kasar Sin Take Ta Kyautata Dangantakar Tattalin Arziki Da Amurka
  • Shirin Tallafinmu Ga Nijeriya A 2025 Zai Kai Ga Asalin Mabukata – Wakilin MDD

“Mutane dubu bakwai da dari bakwai da arba’in da shida sun ragu a fadin jihohi 36 da kuma Babban Birnin Tarayya Abuja daga rajistar masu kada kuri’a zuwa watan Disamba 2022,” in ji ta.

ADVERTISEMENT

A cewar hukumar INEC, ana tsaftace rajistar masu kada kuri’a kafin kowane babban zabe.

A bitar zaben 2023 bayan kammala zabe a watan Disamba na 2024, INEC ta bayyana kalubalen da ke tattare da tsaftace rajistar masu kada kuri’a, duk da ingantuwar tsarin rajistar masu kada kuri’a da aka samu wanda ya kara sabbin masu rajista har guda 12,298,944.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Wani babban batu shi ne, wahalar cire wadanda suka mutu sakamakon gibin bayanan mutuwar a hukumance.

“Matsalolin da ke tattare da bayanan mutuwar jami’ai na ci gaba da yin wahala ga INEC wajen cire wadanda suka mutu rajistar zabe,” in ji hukumar.

Hukumar ta kuma gano matsalar yin rajista sau biyu ko kuma da yawa, wanda aka magance ta hanyar tura na’urar tantance bayanan masu kada kuri’a.

Wannan tsari ya ba da alama tare da cire shari’o’in 2,780,756 na rajista marasa inganci, wanda ke wakiltar kashi 22.6 na duk sabbin masu rajista a fadin kasar nan.

INEC ta kara nuna damuwa game da raguwar fitowar masu kada kuri’a. Zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar dokokin kasar a shekarar 2023, ya samu fitowar kashi 27.5 cikin 100, inda ya ragu da kashi 35.6 a shekarar 2019.

Wasu masu ruwa da tsaki sun alakanta wannan raguwar wani bangare na hauhawar rajistar masu kada kuri’a tare da yin kira da a kara himma wajen tsaftace ta.

Masu ruwa da tsaki a wannan bitar sun ba da shawarar cewa ya kamata INEC ta karfafa hadin gwiwa da hukumomi irinsu hukumar kula da yawan jama’a ta kasa (NPC) da kuma hukumar kula da tantance ‘yan kasa (NIMC) domin tantance wadanda suka mutu.

Akwai kuma kiraye-kirayen a dakatar da mutanen da ba su yi zabe ba a zabuka uku da suka gabata da kuma bukatar su sake sabunta rajistarsu.

“Shawara daya daga cikin wannan bita ita ce a karfafa hadin gwiwa da sauran hukumomi irinsu NIMC da NPC don zakulo wadanda suka rasu a cikin rajista da cire su. Bugu da kari, hukumar za ta iya dakatar da mutanen da ba su yi zabe ba a zabuka uku da suka gabata daga rajistar tare da neman su sabunta rajistarsu,” in ji INEC a bitarta.

INEC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda, Sun Kama Masu Safarar Makamai, Sun Ceto Mutane

LABARAI MASU NASABA

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

June 22, 2026

Mutane 842 Ne Suka Rasa Ransu, Aka Yi Garkuwa Da Sama Da 270 A Watan Mayu – Rahoto

June 21, 2026
PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar  Jamiyyar

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

June 21, 2026
An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

June 21, 2026
An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 21, 2026
Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

June 21, 2026
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 21, 2026
Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

June 21, 2026
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

June 21, 2026
Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.