• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Lashi Takobin Yin Nazari Kan Daukacin Almundahar Zabe

by Abubakar Abba
3 years ago
INEC

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta bayyana cewa, za ta yi nazari kan zarge-zargen cin zarafin masu jefa kuri’a da sauya sakamakon zaben 2023.

INEC ta kuma koka akan sace wasu ma’aikatanta da cin zarafinsu da kuma kashe mata wani ma’aikacinta a lokacin gudanar da zabukan.

  • Da Dumi-Dumi: Gwamna Bala Ya Doke Tsohon Hafsan Sojin Sama Ya Lashe Zaben Bauchi
  • PDP Na Zargin Gwamnan Zamfara Da Yunkurin Murde Sakamakon Karamar Hukumar Maradun

Kwamishinan INEC na kasa kuma shugaban ilimantar da kan masu jefa kuri’a Festus Okoye ne ya sanar da hakan a taron manema labarai a Abuja.

Ya ce, tun farko INEC ta sanar da harin da ‘yan bangar siyasa suka yi wa ofis dinta da ke karamar hukumar Obingwa ta jihar Abia a lokacin tattara sakamakon zaben gwamnoni da na ‘yan majalisar dokoki.

Ya ce, hukumar za ta ci gaba kare mutuncin masu kada kuri’a, inda ya kara da cewa, hukumar ba za ta yi sako -sako wajen daukar mataki ba don binciko zargin almundanar da aka aikata na cin zarafin masu jefa kuri’a ba don yin nazari akai.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kaduna Za Ta Ɗauki Ma’aikatan Lafiya 9,000 Cikin Shekaru 5 – Maiyaki 

Wani Sabon Hari Kan Al’ummar Da Ke Iyaka Da Katsina A Kano Ya Rutsa Da Mata 5

A cewarsa, wasu daga cikin ma’aikatan mu an sace su, wasu an ci zarafin su wasu an kwantar da su a asibiti an kuma hallaka daya.

Sai dai, Okoye ya koka kan yadda aka tayar da hargitsi a wasu wuraren da aka shirya gudanar da zabukan tare da kuma lalata kayan zabe.

Kwamishin ya nuna jin dadin akan yadda aka kara samun inganta ayyukan hukumar musamman wajen tura kayan aiki zuwa rumfunan zabe akan lokaci, inda hakan ya bayar da dama wajen bude rumfunan zabe akan lokaci kamar yadda aka tsara da kuma yadda aka sake inganta na’urar zabe ta BVAS da kuma sauke sakamakon zabe na mazabu daga manhajar IReV.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Kaduna Za Ta Ɗauki Ma’aikatan Lafiya 9,000 Cikin Shekaru 5 – Maiyaki 
Labarai

Gwamnatin Kaduna Za Ta Ɗauki Ma’aikatan Lafiya 9,000 Cikin Shekaru 5 – Maiyaki 

November 10, 2025
Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo
Labarai

Wani Sabon Hari Kan Al’ummar Da Ke Iyaka Da Katsina A Kano Ya Rutsa Da Mata 5

November 10, 2025
Matatun mai
Labarai

Yadda Sojoji Suka Tarwatsa Haramtattun Matatun Mai 14 A Yankin Neja Delta 

November 10, 2025
Next Post
Jakadiyar Birtaniya A Nijeriya Ta Janye Taya Binani Murnar Lashe Zaben Adamawa

Jakadiyar Birtaniya A Nijeriya Ta Janye Taya Binani Murnar Lashe Zaben Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kaduna Za Ta Ɗauki Ma’aikatan Lafiya 9,000 Cikin Shekaru 5 – Maiyaki 

Gwamnatin Kaduna Za Ta Ɗauki Ma’aikatan Lafiya 9,000 Cikin Shekaru 5 – Maiyaki 

November 10, 2025
Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

Wani Sabon Hari Kan Al’ummar Da Ke Iyaka Da Katsina A Kano Ya Rutsa Da Mata 5

November 10, 2025
Matatun mai

Yadda Sojoji Suka Tarwatsa Haramtattun Matatun Mai 14 A Yankin Neja Delta 

November 10, 2025
Jibrin Kofa

Ɗan Majalisar Wakilai, Jibrin Ƙofa Ya Sauya Sheƙa Daga NNPP Zuwa APC

November 10, 2025
Boko haram

Sojoji Sun Fatattaki Boko Haram, Sun Ceto Mutane 86 Da Aka Sace A Borno

November 10, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.