Rundunar Sojin Nijeriya, Runduna ta 6, ta ce jami’anta sun kama wasu da ake zargi da satar mai su 14 tare da kwace sama da lita 20,000 a yankin Neja Delta.
Haka kuma, rundunar ta ce sojoji sun tarwatsa haramtattun matatun mai 14 ba bisa ka’ida ba a lokacin wani samame na musamman a wuraren da ake kyautata tsammanin badaƙalar muggan ayyuka a wuraren.
- Ɗan Majalisar Wakilai, Jibrin Ƙofa Ya Sauya Sheƙa Daga NNPP Zuwa APC
- Sojoji Sun Fatattaki Boko Haram, Sun Ceto Mutane 86 Da Aka Sace A Borno
Hakan na kunshe ne acikin wata sanarwa da Mukaddashin Daraktan Hulda da Jama’a na Rundunar Sojan Runduna ta 6, Jonah Danjuma, ya fitar a Fatakwal a safiyar Litinin.
An cimma wannan nasara ne a wani samame da aka kai tsawon makonni biyu a wasu wuraren da ake zargin ana aikata laifuka a yankin mai arzikin mai, in ji sanarwar.
Rundunar Sojin ta yi alƙawarin ƙara ƙaimi kan tarwatsa duk wata haramtacciyar matata a yankin Neja Delta tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin tsaro.














