• English
  • Business News
Friday, June 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Raba Muhimman Kayyayakin Zabe Don Kammala Zaben Gwamnan Kebbi

by Umar Faruk
2 years ago
in Labarai
0
INEC Ta Raba Muhimman Kayyayakin Zabe Don Kammala Zaben Gwamnan Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mista Festus Okoye, kwamishinan hukumar INEC na kasa mai kula da sashen wayar da kan masu kada kuri’a da watsa labarai, ya tabbatar da cewa hukumar ta shirya tsaf domin gudanar da zaben da ba a kammala ba a duk fadin jihar Kebbi.

Ya bayar da wannan tabbacin ne a lokacin da yake zantawa da ‘yan jarida jim kadan bayan raba muhimman kayyakin ga kananan hukumomin da karasa zaben ya shafa a hedikwatar INEC na jihar da ke Birnin Kebbi a ranar Juma’a.

  • Mun Shirya Tsaf Don Sake Yin Zabe A Jihohin Adamawa, Kebbi– INEC

Za a gudanar da zaben gwamnan da ba a kammala ba a rumfunan zabe 142 da ke fadin kananan hukumomi 20 daga cikin kananan hukumomi 21 na jihar.

Za a sake gudanar da zabuka a yankin Sanatan Kebbi ta Arewa, mazabar tarayya biyu da kuma mazabun ‘yan majalisar dokoki na jihar gudu takwas.

INEC

Labarai Masu Nasaba

Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi

Nijeriya Ce Ta 3 A Manyan Kasashe Masu Karfin Masana’antu 10 Na Afirka

Kwamishinan ya bayyana jin dadinsa cewa hukumar ta kammala rabon kayan zabe masu muhimmanci da suka hada da; takardun zabe, takardar sanya sakamakon zabe da na’urorin BVAS don tantance masu jefa kuri’a a rumfunan da abin ya shafa.

Ya ce, “Hukumar INEC na da hulda da masu ruwa da tsaki da jam’iyyun siyasa daban-daban, kungiyoyin farar hula da kuma kungiyoyi domin tabbatar da an gudanar da zabukan da ba a kammala ba yadda ya dace.”

Hakazalika Kwamishinan dai ya kara da cewa shugabannin hukumomin tsaro sun yi alkawarin cewa su na da jajircewa, iyawa da kuma kayan aiki don tabbatar da an gudanar da dukkan sauran zabuka da ba a kammala a cikin tsaro da kwanciyar hankalin a duk wuraren da abin ya shafa, “Ma’ana jami’an tsaro sun shirya tsaf bisa ga tabbacin da suka baiwa hukumar zabe,” inji mista Festus Okoye.

“A namu bangaren shugaban hukumar ya tura kwamishinonin kasa uku jihar Kebbi saboda yawan zabukan da muke da su a nan, ya kuma tura ma’aikatan da za su jagoranci wannan zabe na musamman.

“Don haka, za mu samu mafi yawan ma’aikatanmu da za su yi aiki a matsayin Shugabannin kula da sanya ido watau turawan zabe, LG Tech da kuma yin ayyuka daban-daban don tabbatar da cewa an gudanar da zabukan cikin nasara.

INEC

“Ba za mu sake yin wani karin zabe ba, za mu kammala zaben nan, don haka a ranar Lahadi ‘yan Kebbi za su iya sanin wanene Gwamnan su kamar kowace jihar ta tarayya,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasa Da Wata Biyu Ya Bar Mulki, Shin Ko Buhari Ya Cika Wa ‘Yan Nijeriya Alkawarin Da Ya Yi Mu Su?

Next Post

Masanin Tattalin Arziki: Kasar Sin Ce Karfin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Related

Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi
Manyan Labarai

Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi

7 minutes ago
Nijeriya Ce Ta 3 A Manyan Kasashe Masu Karfin Masana’antu 10 Na Afirka
Labarai

Nijeriya Ce Ta 3 A Manyan Kasashe Masu Karfin Masana’antu 10 Na Afirka

2 hours ago
nijeriya
Manyan Labarai

Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai

2 hours ago
Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu
Labarai

Cikakken Jerin Sunaye: Tinubu Ya Karrama ‘Yan Nijeriya 102 Don Bukin Ranar Dimokuradiyya Ta 2025

12 hours ago
Zambar Naira Miliyan 55: ICPC Ta Fara Bin Diddigin Dan Kwangilar Dam Din Jihar Filato
Labarai

ICPC Ta Gurfanar Da Ma’aikacin Kotu Bisa Badakalar Naira Miliyan 9.2

13 hours ago
Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu
Manyan Labarai

Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu

17 hours ago
Next Post
Masanin Tattalin Arziki: Kasar Sin Ce Karfin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Masanin Tattalin Arziki: Kasar Sin Ce Karfin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi

Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi

June 13, 2025
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

Darussan Hadisin Aikin Hajjin Manzon Allah S.A.W (2)

June 13, 2025
Nijeriya Ce Ta 3 A Manyan Kasashe Masu Karfin Masana’antu 10 Na Afirka

Nijeriya Ce Ta 3 A Manyan Kasashe Masu Karfin Masana’antu 10 Na Afirka

June 13, 2025
nijeriya

Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai

June 13, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: An Yi Kira Ga Amurka Da Ta Cimma Daidaito Da Sin Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: An Yi Kira Ga Amurka Da Ta Cimma Daidaito Da Sin Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya

June 12, 2025
Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu

Cikakken Jerin Sunaye: Tinubu Ya Karrama ‘Yan Nijeriya 102 Don Bukin Ranar Dimokuradiyya Ta 2025

June 12, 2025
Sin Na Fatan Amurka Ta Yi Hadin Gwiwa Da Ita Don Tabbatar Da Matsayar Da Shugabannin Kasashen Biyu Suka Cimma

Sin Na Fatan Amurka Ta Yi Hadin Gwiwa Da Ita Don Tabbatar Da Matsayar Da Shugabannin Kasashen Biyu Suka Cimma

June 12, 2025
Sin Ta sanya Indonesiya Cikin Tsarin Shiga Kasar Ba Tare Da Biza Ba Na Sa’o’i 240 Da Kara Yawan Kasashen Tsarin Zuwa 55

Sin Ta sanya Indonesiya Cikin Tsarin Shiga Kasar Ba Tare Da Biza Ba Na Sa’o’i 240 Da Kara Yawan Kasashen Tsarin Zuwa 55

June 12, 2025
Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Afirka Sun Yi Alkawarin Karfafa Alaka

Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Afirka Sun Yi Alkawarin Karfafa Alaka

June 12, 2025
Zambar Naira Miliyan 55: ICPC Ta Fara Bin Diddigin Dan Kwangilar Dam Din Jihar Filato

ICPC Ta Gurfanar Da Ma’aikacin Kotu Bisa Badakalar Naira Miliyan 9.2

June 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.