ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Raba Muhimman Kayyayakin Zabe Don Kammala Zaben Gwamnan Kebbi

by Umar Faruk
3 years ago
INEC

Mista Festus Okoye, kwamishinan hukumar INEC na kasa mai kula da sashen wayar da kan masu kada kuri’a da watsa labarai, ya tabbatar da cewa hukumar ta shirya tsaf domin gudanar da zaben da ba a kammala ba a duk fadin jihar Kebbi.

Ya bayar da wannan tabbacin ne a lokacin da yake zantawa da ‘yan jarida jim kadan bayan raba muhimman kayyakin ga kananan hukumomin da karasa zaben ya shafa a hedikwatar INEC na jihar da ke Birnin Kebbi a ranar Juma’a.

  • Mun Shirya Tsaf Don Sake Yin Zabe A Jihohin Adamawa, Kebbi– INEC

Za a gudanar da zaben gwamnan da ba a kammala ba a rumfunan zabe 142 da ke fadin kananan hukumomi 20 daga cikin kananan hukumomi 21 na jihar.

ADVERTISEMENT

Za a sake gudanar da zabuka a yankin Sanatan Kebbi ta Arewa, mazabar tarayya biyu da kuma mazabun ‘yan majalisar dokoki na jihar gudu takwas.

INEC

LABARAI MASU NASABA

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Kwamishinan ya bayyana jin dadinsa cewa hukumar ta kammala rabon kayan zabe masu muhimmanci da suka hada da; takardun zabe, takardar sanya sakamakon zabe da na’urorin BVAS don tantance masu jefa kuri’a a rumfunan da abin ya shafa.

Ya ce, “Hukumar INEC na da hulda da masu ruwa da tsaki da jam’iyyun siyasa daban-daban, kungiyoyin farar hula da kuma kungiyoyi domin tabbatar da an gudanar da zabukan da ba a kammala ba yadda ya dace.”

Hakazalika Kwamishinan dai ya kara da cewa shugabannin hukumomin tsaro sun yi alkawarin cewa su na da jajircewa, iyawa da kuma kayan aiki don tabbatar da an gudanar da dukkan sauran zabuka da ba a kammala a cikin tsaro da kwanciyar hankalin a duk wuraren da abin ya shafa, “Ma’ana jami’an tsaro sun shirya tsaf bisa ga tabbacin da suka baiwa hukumar zabe,” inji mista Festus Okoye.

“A namu bangaren shugaban hukumar ya tura kwamishinonin kasa uku jihar Kebbi saboda yawan zabukan da muke da su a nan, ya kuma tura ma’aikatan da za su jagoranci wannan zabe na musamman.

“Don haka, za mu samu mafi yawan ma’aikatanmu da za su yi aiki a matsayin Shugabannin kula da sanya ido watau turawan zabe, LG Tech da kuma yin ayyuka daban-daban don tabbatar da cewa an gudanar da zabukan cikin nasara.

INEC

“Ba za mu sake yin wani karin zabe ba, za mu kammala zaben nan, don haka a ranar Lahadi ‘yan Kebbi za su iya sanin wanene Gwamnan su kamar kowace jihar ta tarayya,” in ji shi.

INEC
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

MASU ALAKA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Labarai

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
Ra'ayi Riga

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci
Rahotonni

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

July 24, 2026
Next Post
Masanin Tattalin Arziki: Kasar Sin Ce Karfin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Masanin Tattalin Arziki: Kasar Sin Ce Karfin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

LABARAI MASU NASABA

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.