• English
  • Business News
Thursday, June 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Za Ta Dauki Hayar Motocin Sufuri 100,000 Da Jiragen Ruwa 4,200 Don Raba Kayan Zabe – Yakubu

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
INEC Za Ta Dauki Hayar Motocin Sufuri 100,000 Da Jiragen Ruwa 4,200 Don Raba Kayan Zabe – Yakubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da saura kwanaki 66 a yi zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar dattawa, Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya tabbatar da cewa hukumar sa za ta yi amfani da motocin sufuri har 100,000 da kuma jiragen ruwa 4,200 domin raba ma’aikata da kuma kayan zaɓen 2023.

Yakubu ya bayyana haka a lokacin wani ƙwarya-ƙwaryan bukin sa hannu kan yarjejeniyar da INEC ta cimma tare da ƙungiyoyin motocin sufuri da na jiragen ruwa, ranar Talata a Abuja.

  • Kai Wa Ofishoshinmu Hari Na Iya Kawo Cikas Ga Zaben 2023 – INEC

Ya ce INEC za ta yi amfani da su ne domin tabbatar da cewa karakainar raba kayan zaɓe da jami’an zaɓe bai samu wata tangarɗa kafin ranar zaɓe da kuma ranar zaɓen ba.

Shugabannin ƙungiyoyin sufurin da INEC ta ƙulla yarjejeniyar da su, uku ne da su ka haɗa da ƙungiyar direbobi ta NURTW, Kungiyar Masu Motocin Sufuri wato NARTO da kuma Ƙungiyar Mataikatan Jiragen Ruwa, MWUN.

“INEC za ta yi amfani da motoci 100,000, jiragen ruwa 4,200 da kuma ma’aikatan zaɓe miliyan ɗaya.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Soke Yin Jawabi Ga ‘Yan Kasa Na Ranar Dimokuradiyya, Zai Yi Daga Zauren Majalisa

Ɗan Ƙasar Indiya Da Wasu 12 Sun Gurfana A Kotu Kan Satar Wa Dangote Dizal Na Naira Biliyan 4

“Hakan ne ya sa mu ka ƙulla wannan yarjejeniya da ƙungiyoyin sufuri uku domin tabbatar da komai ya tafi daidai a cikin nasara, kamar yadda aka tsara.

INEC

“Waɗannan motoci da jiragen ruwa za su yi karakainar ɗaukar jami’an zaɓe da kayan zaɓe sau biyu kenan a lokacin zaɓen ranar 25 ga Fabrairu da kuma ranar 11 ga Maris, 2023. Za su yi aikin jirga-jirgar kai kayan zaɓe da jami’an zaɓe a dukkanin ƙananan hukumomi 774, mazaɓu 8,809 da kuma rumfunan zaɓe 176,846 da ke faɗin ƙasar nan.

“Za a riƙa yi wa jiragen ruwan da ke ɗauke da kayan aiki kariya da samun rakiyar sojoji ɗauke da makamai a cikin ƙananan jiragen ruwa na yaƙi.”

Yakubu ya bada tabbacin cewa tun ƙarfe 8:30 na safiyar 25 ga Fabrairu, 2023 jami’an zaɓe za su fito domin fara tantance masu jefa ƙuri’a. Sannan kuma ya ce baya ga motoci da jiragen ruwa, INEC za ta yi amfani da Keke NAPEP da babura domin isar da kayan aikin zaɓe cikin kowane lungu.

Daga nan ya umarci shugabannin ƙungiyoyin motocin sufurin su sani cewa wannan yarjejeniyar da su ka sa hannu, tamkar rantsuwa ce cewa ba za su aikata ba daidai ba.

INEC

Ya ce su ja kunnen direbobin su kada su nuna son kai ko fifita wani ɗan takara ko wata jam’iyya. Kuma kada su haɗa kai da jami’an tsaron da za a riƙa haɗa su aikin kariya da tsaro su yi amfani da kayan zaɓe ta hanyar da ba ta dace ba.

Shugaban NURTW, Tajuddeen Baruwa, ya tabbatar wa INEC cewa wannan yarjejeniyar da su ka sa wa hannu sun amince alƙawari ne cewa za su yi aiki tsakani da Allah domin bai wa ƙasar su gudummawar tabbatar da an gudanar da zaɓukan 2023 cikin kwanciyar hankali.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Osinbajo Da Tinubu Sun Yi Ganawar Sirri Kan Shirin Zaben 2023

Next Post

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kwace Dala 899,900 Da Naira Miliyan 304 A Wurin Ahmed Idris

Related

haraji
Labarai

Tinubu Ya Soke Yin Jawabi Ga ‘Yan Kasa Na Ranar Dimokuradiyya, Zai Yi Daga Zauren Majalisa

2 hours ago
Dangote
Labarai

Ɗan Ƙasar Indiya Da Wasu 12 Sun Gurfana A Kotu Kan Satar Wa Dangote Dizal Na Naira Biliyan 4

3 hours ago
Filato
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutane 8 A Jihar Filato

5 hours ago
Duk Da Cewa Wike Ba Ɗan APC Ba Ne Amma Muna Jin Daɗin Aikin sa – Tinubu
Manyan Labarai

Duk Da Cewa Wike Ba Ɗan APC Ba Ne Amma Muna Jin Daɗin Aikin sa – Tinubu

7 hours ago
Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna
Ra'ayi Riga

Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna

9 hours ago
Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Soke Faretin Ranar Dimokuraɗiyya, Tinubu Zai Yi Wa ‘Yan Ƙasa Jawabi 

11 hours ago
Next Post
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kwace Dala 899,900 Da Naira Miliyan 304 A Wurin Ahmed Idris

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kwace Dala 899,900 Da Naira Miliyan 304 A Wurin Ahmed Idris

LABARAI MASU NASABA

Yadda Kasar Sin Ta Zo Da Sabon Salon Zamanantar Da Sashen Jigilar Kayayyaki

Yadda Kasar Sin Ta Zo Da Sabon Salon Zamanantar Da Sashen Jigilar Kayayyaki

June 11, 2025
haraji

Tinubu Ya Soke Yin Jawabi Ga ‘Yan Kasa Na Ranar Dimokuradiyya, Zai Yi Daga Zauren Majalisa

June 11, 2025
An Gudanar Da Taron Ministoci Masu Daidaita Ayyukan Da Aka Amince Yayin Taron FOCAC

An Gudanar Da Taron Ministoci Masu Daidaita Ayyukan Da Aka Amince Yayin Taron FOCAC

June 11, 2025
Dangote

Ɗan Ƙasar Indiya Da Wasu 12 Sun Gurfana A Kotu Kan Satar Wa Dangote Dizal Na Naira Biliyan 4

June 11, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Kaso Kusan 80% Sun Soki Musabbabin Barkewar Tarzoma A Amurka

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Kaso Kusan 80% Sun Soki Musabbabin Barkewar Tarzoma A Amurka

June 11, 2025
Kasuwancin Sin Da Afirka Ya Habaka Cikin Hanzari A Shekaru 25 Da Suka Gabata

Kasuwancin Sin Da Afirka Ya Habaka Cikin Hanzari A Shekaru 25 Da Suka Gabata

June 11, 2025
Filato

‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutane 8 A Jihar Filato

June 11, 2025
He Lifeng Ya Bukaci Amurka Da Ta Warware Takaddamar Cinikayya Da Sin Ta Hanyar Tattaunawa Da Hadin Gwiwa

He Lifeng Ya Bukaci Amurka Da Ta Warware Takaddamar Cinikayya Da Sin Ta Hanyar Tattaunawa Da Hadin Gwiwa

June 11, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Afrika

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Afrika

June 11, 2025
Duk Da Cewa Wike Ba Ɗan APC Ba Ne Amma Muna Jin Daɗin Aikin sa – Tinubu

Duk Da Cewa Wike Ba Ɗan APC Ba Ne Amma Muna Jin Daɗin Aikin sa – Tinubu

June 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.