• English
  • Business News
Tuesday, June 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Za Ta Dauki Hayar Motocin Sufuri 100,000 Da Jiragen Ruwa 4,200 Don Raba Kayan Zabe – Yakubu

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
INEC Za Ta Dauki Hayar Motocin Sufuri 100,000 Da Jiragen Ruwa 4,200 Don Raba Kayan Zabe – Yakubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da saura kwanaki 66 a yi zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar dattawa, Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya tabbatar da cewa hukumar sa za ta yi amfani da motocin sufuri har 100,000 da kuma jiragen ruwa 4,200 domin raba ma’aikata da kuma kayan zaɓen 2023.

Yakubu ya bayyana haka a lokacin wani ƙwarya-ƙwaryan bukin sa hannu kan yarjejeniyar da INEC ta cimma tare da ƙungiyoyin motocin sufuri da na jiragen ruwa, ranar Talata a Abuja.

  • Kai Wa Ofishoshinmu Hari Na Iya Kawo Cikas Ga Zaben 2023 – INEC

Ya ce INEC za ta yi amfani da su ne domin tabbatar da cewa karakainar raba kayan zaɓe da jami’an zaɓe bai samu wata tangarɗa kafin ranar zaɓe da kuma ranar zaɓen ba.

Shugabannin ƙungiyoyin sufurin da INEC ta ƙulla yarjejeniyar da su, uku ne da su ka haɗa da ƙungiyar direbobi ta NURTW, Kungiyar Masu Motocin Sufuri wato NARTO da kuma Ƙungiyar Mataikatan Jiragen Ruwa, MWUN.

“INEC za ta yi amfani da motoci 100,000, jiragen ruwa 4,200 da kuma ma’aikatan zaɓe miliyan ɗaya.

Labarai Masu Nasaba

Shin Rashin Nasara Ya Rage Damar Yamal Na Ballon d’Or?

Gwamnatin Bauchi Ta Buɗe Sabon Tsarin Neman Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

“Hakan ne ya sa mu ka ƙulla wannan yarjejeniya da ƙungiyoyin sufuri uku domin tabbatar da komai ya tafi daidai a cikin nasara, kamar yadda aka tsara.

INEC

“Waɗannan motoci da jiragen ruwa za su yi karakainar ɗaukar jami’an zaɓe da kayan zaɓe sau biyu kenan a lokacin zaɓen ranar 25 ga Fabrairu da kuma ranar 11 ga Maris, 2023. Za su yi aikin jirga-jirgar kai kayan zaɓe da jami’an zaɓe a dukkanin ƙananan hukumomi 774, mazaɓu 8,809 da kuma rumfunan zaɓe 176,846 da ke faɗin ƙasar nan.

“Za a riƙa yi wa jiragen ruwan da ke ɗauke da kayan aiki kariya da samun rakiyar sojoji ɗauke da makamai a cikin ƙananan jiragen ruwa na yaƙi.”

Yakubu ya bada tabbacin cewa tun ƙarfe 8:30 na safiyar 25 ga Fabrairu, 2023 jami’an zaɓe za su fito domin fara tantance masu jefa ƙuri’a. Sannan kuma ya ce baya ga motoci da jiragen ruwa, INEC za ta yi amfani da Keke NAPEP da babura domin isar da kayan aikin zaɓe cikin kowane lungu.

Daga nan ya umarci shugabannin ƙungiyoyin motocin sufurin su sani cewa wannan yarjejeniyar da su ka sa hannu, tamkar rantsuwa ce cewa ba za su aikata ba daidai ba.

INEC

Ya ce su ja kunnen direbobin su kada su nuna son kai ko fifita wani ɗan takara ko wata jam’iyya. Kuma kada su haɗa kai da jami’an tsaron da za a riƙa haɗa su aikin kariya da tsaro su yi amfani da kayan zaɓe ta hanyar da ba ta dace ba.

Shugaban NURTW, Tajuddeen Baruwa, ya tabbatar wa INEC cewa wannan yarjejeniyar da su ka sa wa hannu sun amince alƙawari ne cewa za su yi aiki tsakani da Allah domin bai wa ƙasar su gudummawar tabbatar da an gudanar da zaɓukan 2023 cikin kwanciyar hankali.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Osinbajo Da Tinubu Sun Yi Ganawar Sirri Kan Shirin Zaben 2023

Next Post

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kwace Dala 899,900 Da Naira Miliyan 304 A Wurin Ahmed Idris

Related

Shin Rashin Nasara Ya Rage Damar Yamal Na Ballon d’Or?
Labarai

Shin Rashin Nasara Ya Rage Damar Yamal Na Ballon d’Or?

3 hours ago
Gwamnatin Bauchi Ta Buɗe Sabon Tsarin Neman Ƙirƙirar Sabbin Masarautu
Labarai

Gwamnatin Bauchi Ta Buɗe Sabon Tsarin Neman Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

4 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kai Farmaki Kwara, Sun Kashe Mutum 1, Sun Ƙona Gidaje
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kai Farmaki Kwara, Sun Kashe Mutum 1, Sun Ƙona Gidaje

5 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Laifi 27 A Kaduna
Tsaro

Ƴansanda Sun Kama Masu Laifi 27 A Kaduna

7 hours ago
Matawalle: Kofarmu Abude Take Idan Gwamna Dauda Lawal Na San Shigowa Jamiyyar APC
Labarai

Matawalle: Kofarmu Abude Take Idan Gwamna Dauda Lawal Na San Shigowa Jamiyyar APC

10 hours ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 11 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina

13 hours ago
Next Post
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kwace Dala 899,900 Da Naira Miliyan 304 A Wurin Ahmed Idris

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kwace Dala 899,900 Da Naira Miliyan 304 A Wurin Ahmed Idris

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Firaministan Sin Ya Gana Da Ministar Kudin Birtaniya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Gana Da Ministar Kudin Birtaniya

June 9, 2025
An Kaddamar Da Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka A London

An Kaddamar Da Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka A London

June 9, 2025
Shin Rashin Nasara Ya Rage Damar Yamal Na Ballon d’Or?

Shin Rashin Nasara Ya Rage Damar Yamal Na Ballon d’Or?

June 9, 2025
Kididiga Ta Nuna Yadda Kasar Sin Ke Samun Bunkasar Tattalin Arzikin Teku

Kididiga Ta Nuna Yadda Kasar Sin Ke Samun Bunkasar Tattalin Arzikin Teku

June 9, 2025
Kasashen Da Sin Ta Bai Wa Jama’arsu Izinin Shiga Kasar Ba Tare Da Biza Ba Ya Karu Zuwa 47

Kasashen Da Sin Ta Bai Wa Jama’arsu Izinin Shiga Kasar Ba Tare Da Biza Ba Ya Karu Zuwa 47

June 9, 2025
Gwamnatin Bauchi Ta Buɗe Sabon Tsarin Neman Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnatin Bauchi Ta Buɗe Sabon Tsarin Neman Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

June 9, 2025
Ma’aunin Farashin Kayan Masarufi Na Watan Mayu A Kasar Sin Ya Ragu Da Kaso 0.1 Bisa Dari

Ma’aunin Farashin Kayan Masarufi Na Watan Mayu A Kasar Sin Ya Ragu Da Kaso 0.1 Bisa Dari

June 9, 2025
Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Gargadi Mahukuntan Taiwan Game Da Sayen Makamai Daga Amurka

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Gargadi Mahukuntan Taiwan Game Da Sayen Makamai Daga Amurka

June 9, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Farmaki Kwara, Sun Kashe Mutum 1, Sun Ƙona Gidaje

Ƴan Bindiga Sun Kai Farmaki Kwara, Sun Kashe Mutum 1, Sun Ƙona Gidaje

June 9, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Laifi 27 A Kaduna

Ƴansanda Sun Kama Masu Laifi 27 A Kaduna

June 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.