• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Za Ta Dauki Hayar Motocin Sufuri 100,000 Da Jiragen Ruwa 4,200 Don Raba Kayan Zabe – Yakubu

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
INEC Za Ta Dauki Hayar Motocin Sufuri 100,000 Da Jiragen Ruwa 4,200 Don Raba Kayan Zabe – Yakubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da saura kwanaki 66 a yi zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar dattawa, Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya tabbatar da cewa hukumar sa za ta yi amfani da motocin sufuri har 100,000 da kuma jiragen ruwa 4,200 domin raba ma’aikata da kuma kayan zaɓen 2023.

Yakubu ya bayyana haka a lokacin wani ƙwarya-ƙwaryan bukin sa hannu kan yarjejeniyar da INEC ta cimma tare da ƙungiyoyin motocin sufuri da na jiragen ruwa, ranar Talata a Abuja.

  • Kai Wa Ofishoshinmu Hari Na Iya Kawo Cikas Ga Zaben 2023 – INEC

Ya ce INEC za ta yi amfani da su ne domin tabbatar da cewa karakainar raba kayan zaɓe da jami’an zaɓe bai samu wata tangarɗa kafin ranar zaɓe da kuma ranar zaɓen ba.

Shugabannin ƙungiyoyin sufurin da INEC ta ƙulla yarjejeniyar da su, uku ne da su ka haɗa da ƙungiyar direbobi ta NURTW, Kungiyar Masu Motocin Sufuri wato NARTO da kuma Ƙungiyar Mataikatan Jiragen Ruwa, MWUN.

“INEC za ta yi amfani da motoci 100,000, jiragen ruwa 4,200 da kuma ma’aikatan zaɓe miliyan ɗaya.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

“Hakan ne ya sa mu ka ƙulla wannan yarjejeniya da ƙungiyoyin sufuri uku domin tabbatar da komai ya tafi daidai a cikin nasara, kamar yadda aka tsara.

INEC

“Waɗannan motoci da jiragen ruwa za su yi karakainar ɗaukar jami’an zaɓe da kayan zaɓe sau biyu kenan a lokacin zaɓen ranar 25 ga Fabrairu da kuma ranar 11 ga Maris, 2023. Za su yi aikin jirga-jirgar kai kayan zaɓe da jami’an zaɓe a dukkanin ƙananan hukumomi 774, mazaɓu 8,809 da kuma rumfunan zaɓe 176,846 da ke faɗin ƙasar nan.

“Za a riƙa yi wa jiragen ruwan da ke ɗauke da kayan aiki kariya da samun rakiyar sojoji ɗauke da makamai a cikin ƙananan jiragen ruwa na yaƙi.”

Yakubu ya bada tabbacin cewa tun ƙarfe 8:30 na safiyar 25 ga Fabrairu, 2023 jami’an zaɓe za su fito domin fara tantance masu jefa ƙuri’a. Sannan kuma ya ce baya ga motoci da jiragen ruwa, INEC za ta yi amfani da Keke NAPEP da babura domin isar da kayan aikin zaɓe cikin kowane lungu.

Daga nan ya umarci shugabannin ƙungiyoyin motocin sufurin su sani cewa wannan yarjejeniyar da su ka sa hannu, tamkar rantsuwa ce cewa ba za su aikata ba daidai ba.

INEC

Ya ce su ja kunnen direbobin su kada su nuna son kai ko fifita wani ɗan takara ko wata jam’iyya. Kuma kada su haɗa kai da jami’an tsaron da za a riƙa haɗa su aikin kariya da tsaro su yi amfani da kayan zaɓe ta hanyar da ba ta dace ba.

Shugaban NURTW, Tajuddeen Baruwa, ya tabbatar wa INEC cewa wannan yarjejeniyar da su ka sa wa hannu sun amince alƙawari ne cewa za su yi aiki tsakani da Allah domin bai wa ƙasar su gudummawar tabbatar da an gudanar da zaɓukan 2023 cikin kwanciyar hankali.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Osinbajo Da Tinubu Sun Yi Ganawar Sirri Kan Shirin Zaben 2023

Next Post

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kwace Dala 899,900 Da Naira Miliyan 304 A Wurin Ahmed Idris

Related

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Da ɗumi-ɗuminsa

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

4 hours ago
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a
Labarai

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

5 hours ago
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson
Labarai

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

6 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

9 hours ago
Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas
Labarai

Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas

12 hours ago
Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos
Labarai

Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos

13 hours ago
Next Post
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kwace Dala 899,900 Da Naira Miliyan 304 A Wurin Ahmed Idris

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kwace Dala 899,900 Da Naira Miliyan 304 A Wurin Ahmed Idris

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.