• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Inuwa Ya Bai Wa ‘Yan Kasuwan Gombe Kyautar Naira Miliyan 500 Don Karfafa Kasuwancinsu 

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Inuwa

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya kaddamar da rabon Naira miliyan dari biyar (N500,000,000) a matsayin tallafi ga kungiyoyin ‘yan kasuwa daban-daban a Jihar Gombe don taimaka musu wajen sake inganta sana’o’i da kasuwancin su da kuma shawo kan matsalar tabarbarewar tattalin arziki da annobar Korona ta haifar. 

 

Wannan karimcin na zuwa ne a karkashin shirin farfado da tattalin arzikin Jihar Gombe na COVID-19 da ake kira GO-CARES, wanda shirin tallafi ne na gwamnatin jihar.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe DPO Da Wani Dan Sanda A Zamfara

Da ya ke jawabi a wajen bikin kaddamar da shirin, gwamnan yakce, gwamnatin sa ta himmatu matuka wajen magance kalubalen zamantakewa da tattalin arziki da suka addabi al’ummar jihar wanda shi ne dalilin kafa gidauniyar farfado da tattalin arzikin Nijeriya wato NG-CARES na Gwamnatin Tarayya a Jihar Gombe inda aka ware sama da Naira biliyan 8 da miliyan 500 don tallafawa magidanta 288,700 da manoma da masu kananan sana’o’i a lungu da sako na jihar domin dakile barnar da cutar Korona ta yi ga tattalin arzikin kasa da rayuwar al’ummar duniya.

Inuwa

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

Ya ce, tun bayan kaddamar da shirin a watan Yulin shekarar da ta gabata, shirin na GO-CARES ya kashe kimanin Naira biliyan 3 da miliyan 400 ta hanyar ayyuka daban-daban da kuma tallafin daya kai ga dubban iyalai da ‘yan kasuwa masu rauni.

 

“Ya zuwa yanzu, ‘yan asalin Jihar Gombe dubu 147 da 666 ne suka ci gajiyar wannan shirin na GO-CARES kuma za a sanya karin wassu da dama nan gaba. Namu tallafi ne ba rance ba, kuma rabon wannan makudan kudade shaida ce ta yadda muke daukar sana’o’i da muhimmanci saboda irin rawar da suke takawa wajen ci gaban jihar mu”.

 

Gwamnan ya bayyana cewa ajandar ci gaban da gwamnatin sa ke aiwatarwa ta hanyar zurfafa zuba jari a fannin samar da ababen more rayuwa da samar da ci gaban jama’a ya samar da yanayi mai kyau ga ‘yan kasuwa, inda ya bada misali da hanyoyi a rukunin masana’antu na Nasarawo da babbar kasuwar Gombe da fitulun hanya masu amfani da hasken rana da inganta tsaro da sauran su.

 

Tun da farko a jawabin sa na maraba, kwamishinan ciniki, masana’antu da yawon shakatawa, Hon. Nasiru Aliyu ya ce, gwamnatin Inuwa zata ci gaba da samar da yanayi mai kyau ga ‘yan kasuwa don dawo da martabar kasuwanci.

 

Shi ma a nasa jawabin, kwamishinan Matasa Hon. Abubakar Aminu Musa, ya ce shirin na GO-CARES ya ceto iyalai da ‘yan kasuwa da dama a fadin jihar ta hanyar tsare-tsaren sa daban-daban, inda ya bukaci wadanda suka ci gajiyar shirin su bada goyon bayan ci gaba da shirin ta hanyar sake zabar Gwamna Inuwa Yahaya a karo na biyu.

 

Da suke jawabi a madadin ‘yan kasuwan da suka amfana, Alhaji Sunusi Abdullahi Mai Agogo da Shugaban kungiyar ‘yan kasuwa kafa waje Alhaji Uba Abdullahi da Shugabar Mata ‘yan Kasuwa Dr. Eliza Danladi da Shugaban hadin kan kungiyar ‘yan kasuwa ta Amalgamated, Alh. Abba Bill Gates, sukace Gwamna Inuwa ya cika alkawuran daya dauka na tallafawa ‘yan kasuwa, suna masu godiya bisa wannan karimcin, tare da bada tabbacin yin amfani da tallafin yadda ya kamata.

Inuwa

Sun kuma yi alkawarin ci gaba da bai wa gwamnan goyon baya, tare da yi masa alkawarin zasu ramawa kura aniyar ta a zabe mai zuwa domin dorewar ayyukan raya ƙasa da kuma maslahar Jihar Gombe.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Manyan Labarai

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Manyan Labarai

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Next Post
Tafarkin Sin Na Zamanantar Da Kanta Zai Amfani Kasashe Masu Tasowa

Tafarkin Sin Na Zamanantar Da Kanta Zai Amfani Kasashe Masu Tasowa

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.