• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

IPMAN Ta Bayyana Dalilin Rashin Fara Sayen Man Fetur Daga Matatar Dangote

by Bello Hamza and Sulaiman
12 months ago
Matatar dangote

Biyo bayan sabuwar takaddama na sayen tataccen mai daga matatar Dangote, kungiyar dillan mai ta kasa IPMAN, ta sanar da cewa, ta na kan tattaunawa da matatar Dangote, dangane da fara sayen mai, daga matatar ta Dangote.

Shugaban rukunin matatar man Dangote Alhaji Aliko Dangote, ya yi zargin cewa, kamfanin kula da albarkatun main a kasa NNPCL, tare da sauran masu ruwa da tsaki, suna shigo da man daga wasu kasashen duniya, suna kuma kin sayen wanda matatarsa ke tacewa.

  • Karin Kayayyaki Daga Kasashe Mafi Karancin Ci Gaba Sun Shiga Kasuwar Kasar Sin Ta Bikin CIIE
  • Zargin Cin Zarafin Likita: Gwamna Yusuf Ya Roki Likitoci Su Bayar Da Kofar Sulhu

Dangote ya kara da cewa, matatarsa, na da karfin da za ta iya samar da tataccen man lita miliyan 500.

Sai dai, a martanin da mai magana da yawun IPMAN na kasa Cif Chinedu Ukadike, ya bayyana cewa, kungiyar ba ta riga ta sayo man daga matatar Dangote ba, domin har yanzu, ana ci gaba da tattaunawa a kan batun.

A cewarsa Chinedu,“Har yanzu, bamu karbi kayan daga matatar man ta Dangote ba, amma ana ci gaba da tattaunawa za mu nkuma sanar idan mun fara karbar kayan daga matatar.”

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025, Kamfanin Nestlé Pure Life

A daya bangaren Chinedu ya bayyana cewa, karin farashin mai da kamfanin NNPCL bayan kwanuka biyu, ba abin mamaki bane duba da yadda kasuwar ta kasance.

Sai dai, duk da karin Naira 30 na kowacce Litar mai daya, wanda ya kai kaso 3 a cikin dari zuwa Naira 1, 060 na kowacce lita daya a Abuja, dilallan man sun ci gaba da sayar da man a watan Okotobar 2024 a kan farasahin da take sayarwa.

Wani bincike da Jaridar Banguard ta gudanar ya nuna cewa, manyan dillalan man kamar su, Conoil and TotalEnergies, sun ci gaba da sayar da man su a kan farashin Naira 1,109, NIPCO akan farshin Naira N1,115, Adoba Plc a kan Naira N1,125, inda kuma akasarin dilalan man, ke sayar da man a kan Naira 1,150 – N1,230.

A kwannan baya ne NNPC ya kara farashin wanda ya kai kashi 14.8 a ranar 9 ga watan Okotobar, 2024, inda karin farashin man ya kai daga Naira 897 zuwa Naira to 1, 030 na kowacce lita daya, bayan cire tallafin mai da gwamnatin tarayya ta yi.

Wannan karin ya sabawa tunanin yarjejiya a tsakanin gwamnatin tarayya da matatar man Dangote, na sayar da danyen mai a farashin Naira mai makon da farashin dala wanda hakan ya sanya farashin ya fara raguwa a ranar 1 ga watan Oktobar 2024.

Karin na kwanan nan, da aka yi a ranar 3 ga watan Satumbar 2024 ya faru ne, bayan NNPC, ya kara farashin litar man zuwa kashi 45, inda farashin ya karu daga Naira 617 zuwa Naira to 897 na kowacce litar man daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria
Tattalin Arziki

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

October 25, 2025
Tattalin Arziki

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025, Kamfanin Nestlé Pure Life

October 25, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA
Tattalin Arziki

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Next Post
Noma

Harajin "VAT" Zai Kara Wa Al'ummar Kasar Nan Kuncin Rayuwa Ne Kawai - Gambo Danpass

LABARAI MASU NASABA

Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025
COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025
Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa

Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.