ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

IPMAN Ta Bayyana Dalilin Rashin Fara Sayen Man Fetur Daga Matatar Dangote

by Bello Hamza and Sulaiman
1 year ago
Matatar dangote

Biyo bayan sabuwar takaddama na sayen tataccen mai daga matatar Dangote, kungiyar dillan mai ta kasa IPMAN, ta sanar da cewa, ta na kan tattaunawa da matatar Dangote, dangane da fara sayen mai, daga matatar ta Dangote.

Shugaban rukunin matatar man Dangote Alhaji Aliko Dangote, ya yi zargin cewa, kamfanin kula da albarkatun main a kasa NNPCL, tare da sauran masu ruwa da tsaki, suna shigo da man daga wasu kasashen duniya, suna kuma kin sayen wanda matatarsa ke tacewa.

  • Karin Kayayyaki Daga Kasashe Mafi Karancin Ci Gaba Sun Shiga Kasuwar Kasar Sin Ta Bikin CIIE
  • Zargin Cin Zarafin Likita: Gwamna Yusuf Ya Roki Likitoci Su Bayar Da Kofar Sulhu

Dangote ya kara da cewa, matatarsa, na da karfin da za ta iya samar da tataccen man lita miliyan 500.

ADVERTISEMENT

Sai dai, a martanin da mai magana da yawun IPMAN na kasa Cif Chinedu Ukadike, ya bayyana cewa, kungiyar ba ta riga ta sayo man daga matatar Dangote ba, domin har yanzu, ana ci gaba da tattaunawa a kan batun.

A cewarsa Chinedu,“Har yanzu, bamu karbi kayan daga matatar man ta Dangote ba, amma ana ci gaba da tattaunawa za mu nkuma sanar idan mun fara karbar kayan daga matatar.”

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

A daya bangaren Chinedu ya bayyana cewa, karin farashin mai da kamfanin NNPCL bayan kwanuka biyu, ba abin mamaki bane duba da yadda kasuwar ta kasance.

Sai dai, duk da karin Naira 30 na kowacce Litar mai daya, wanda ya kai kaso 3 a cikin dari zuwa Naira 1, 060 na kowacce lita daya a Abuja, dilallan man sun ci gaba da sayar da man a watan Okotobar 2024 a kan farasahin da take sayarwa.

Wani bincike da Jaridar Banguard ta gudanar ya nuna cewa, manyan dillalan man kamar su, Conoil and TotalEnergies, sun ci gaba da sayar da man su a kan farashin Naira 1,109, NIPCO akan farshin Naira N1,115, Adoba Plc a kan Naira N1,125, inda kuma akasarin dilalan man, ke sayar da man a kan Naira 1,150 – N1,230.

A kwannan baya ne NNPC ya kara farashin wanda ya kai kashi 14.8 a ranar 9 ga watan Okotobar, 2024, inda karin farashin man ya kai daga Naira 897 zuwa Naira to 1, 030 na kowacce lita daya, bayan cire tallafin mai da gwamnatin tarayya ta yi.

Wannan karin ya sabawa tunanin yarjejiya a tsakanin gwamnatin tarayya da matatar man Dangote, na sayar da danyen mai a farashin Naira mai makon da farashin dala wanda hakan ya sanya farashin ya fara raguwa a ranar 1 ga watan Oktobar 2024.

Karin na kwanan nan, da aka yi a ranar 3 ga watan Satumbar 2024 ya faru ne, bayan NNPC, ya kara farashin litar man zuwa kashi 45, inda farashin ya karu daga Naira 617 zuwa Naira to 897 na kowacce litar man daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Tattalin Arziki

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

November 7, 2025
Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

November 7, 2025
Tattalin Arziki

Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho

November 7, 2025
Next Post
Noma

Harajin "VAT" Zai Kara Wa Al'ummar Kasar Nan Kuncin Rayuwa Ne Kawai - Gambo Danpass

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
'yansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

November 12, 2025
Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

November 12, 2025
Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

November 12, 2025
Majalisar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Bisa Zargin Rashin Ɗa’a

Majalisar Jihar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Kan Laifin Rashin Ɗa’a

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.