• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Irin Babban Taron LEADERSHIP ‘Yan Nijeriya Ke Bukata

by Leadership Hausa
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Irin Babban Taron LEADERSHIP ‘Yan Nijeriya Ke Bukata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban taron LEADERSHIP da aka yi kwanan nan ya amsa sunansa, inda aka hada gwaraza wadanda suka yi fice a fannonin bunkasa rayuwar al’umma daban- daban.Taron ya samar da  wata dama ta tattaunawa tare da musayar ra’ayoyi a kan yadda Nijeriya za ta ci gaba.

Wasu ra’ayoyin da aka gabatar a wurin taron sun tayar da kura da kuma fito da hanyoyin magance matsalolin da aka fito da su. An kuma gano cewa, musabbabin wasu matsalolin sun taso ne daga tsare-tsaren gwamnati da kuma yadda ake aiwatar da wasu tsare-tsaren.

  • Ci Gaban Kasar Sin Na Ingiza Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya
  • Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL

Babban bako mai jawabi a taron, Farfesa Kingsley Moghalu, ya fara daukar hankalin mahalarta taron inda ya bayyana cewa, tattalin arzikin kasar nan na cikin garari, don tabbatar da ikirarinsa ya yi nuni da wasu kurakuran da ke cikin manufofin tattalin arziki na Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, a cewarsa wasu manufofin ba a yi cikakken nazari da tunani ba kafin a aiwatar da su. Ya bayar da misalin cire tallafin man fetur da kuma yadda gwamnati ta cire hannu a kan samar wa Naira daraja, da kuma jinkiri da gwamnatin ta yi na nada gwamnan babban bankin Nijeriya da  kwamitin da gwamnati ta kafa don lura da tsarin tafiyar da tattalin arzikin kasa musamman  ma abin da ya shafi darajar Naira.

A ra’ayinsa, karyewar da tattalin arzikin ya yi zai iya kaiwa shekara uku zuwa biyar kafin ya iya farfadowa. A nasa martanin, Ministan Yada Labarai, Alhaji Mohammed Idris, wanda ya wakilci shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, bai yi wata-wata ba wajen mayar wa da Farfesan  da martani, inda ya ki amincewa da bayanin cewar wai tattalin arzikin Nijeriya na cikin garari amma kuma ya yarda da cewa tattalin arzikin Nijeriya yana fuskantar manyan matsalolin da aka dade ba a ga irinsu ba. A ra’ayin Ministan, dukkan matsalolin da ake fuskanta za su wuce a cikin shekara daya ba kamar shekara uku zuwa biyar ba yadda Farfesan ya yi hasashe.

A  ra’ayin wannan jaridar, gardamar da ke tsakanin wadannan manyan mutanen a kan wannan lamari da ke da muhimmanci a kan abin da ya shafi jin dadin al’ummar Nijeriya ba shi da wani muhimmanci a kan yadda dukkan su suka yarda da cewa a kwai gaggarumin aiki in har ana son fitar da kasar nan daga cikin halin kuncin da al’ummarta ke ciki.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

Ko tattalin arzikin kasa na cikin garari ko kuma yana fuskantar matsaloli babban abin da ya shafi talaka a Nijeriya  da ke a gaban sa shi ne yadda zai  kai wa bakin salati a kullum in garin Allah ya waye, a daidai lokacin da ake fuskantar matsalolin tattalin arziki ta fuskoki da dama, ga kuma yadda aka mayar da dala  a matsayin jagora a dukkan harkokin saye da sayarwa na kasar nan. Wannan ne ya sa a halin yanzu ake sayar da dala a kan kusan naira 1,500. A kan hakan ko tattalin arzikin Nijeriya na cikin gararin ko kuma yana cikin tsaka mai wuyan wannan ba wani abu mai muhimmanci ba ne ga talakan Nijeriya.

A wannan lokaci lamarin tsaron rayuwa da dukiyoyin al’umma wani abu ne da ke bukatar taimako daga Allah. Wannan ya zama hakan ne domin ‘yan siyasar da kuma jami’an tsaron da ya kamata su dauki matakin kare al’umma sun rasa yadda za su yi kusan basu da wata dabara ta kare al’umma, wannann wani abin kunya ne musamman ganin yadda lamarin yake neman kunyata Nijeriya a idon kasashen duniya.

A halin yanzu kuma a bayyana yake nuna cewa, karancin abinci yana barazana ga al’ummar Nijeriya wanda tuni aka ayyana hakan a matsayin hedikwatar talauci ta duniya, wannan abin takaici ne kwarai da gaske.Wasu kuma na bayyana cewa, a Nijeriya ba wai babu kayan abinci ba ne amma kudin sayen abinci ne suka zama matsala ga mutane, duk dai yadda ka fuskanci lamarin, gidaje da dama na fuskantar matsala a kokarin ciyar da kansu a wannan lokacin da ake ciki. Mutanen ba su damu da abin da ya haifar da matsalar ba, abin da suke fata shi ne al’amurra su dawo daidai yadda ya kamata.

Lamarin wutar lantarki ya kara kazancewa, sauran hanyoyin samun makamashi kuma kamar kalanzir da gas sun zama sai wane da wane. Ba abin da ya shafi su na matsalar da tattalin arzikin Nijeriyan ke fuskanta abin da ake bukata shi ne al’ummarra su dawo yadda aka san su a da.

A shekarar 2023, kungiyar masu masana’antu ta kasa ta bayyana cewa, kamfanoni fiye da 335 suke gab da rufewa yayin da kuma kamfanoni fiye da 767 suka durkushe. Har zuwa yanzu masana na ci gaba da kididdiga tare da tattara alkalumma na marasa aiki a Nijeriya da kuma yadda tattalin arzikin kasa ke kara karyewa a kullum. Suna neman a yi wani abu mai muhimmanci don magance lamarin wanda ba karamin barazana ba ne ga tattalin arzikn Nijeriya.

Mun yarda da ra’ayin Moghalu na cewa, majalisar tarayya ta fi karkata ga biyan bukatun ‘yan siyasa a kudure-kudurenta. A ra’ayinmu lallai ya kamata a yi gyara a wannan lamarin.

A ra’ayinmu, abin da ‘yan Nijeriya ke bukata a halin yanzu shi ne a samar musu da abinci a kan farashi mai sauki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tallafin Da Amurka Ta Baiwa Gaza Wasan Kwaikwayo Ne

Next Post

Bayan Sace Dalibai, Mata ‘Yan Hijira Da Almajirai…

Related

‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

5 hours ago
Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara
Manyan Labarai

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

1 day ago
Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin
Manyan Labarai

Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin

1 day ago
Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano
Manyan Labarai

Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano

2 days ago
Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

2 days ago
Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II
Manyan Labarai

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

2 days ago
Next Post
Bayan Sace Dalibai, Mata ‘Yan Hijira Da Almajirai…

Bayan Sace Dalibai, Mata ‘Yan Hijira Da Almajirai…

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

August 8, 2025
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

August 8, 2025
Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

August 8, 2025
Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

August 8, 2025
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

August 8, 2025
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

August 8, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

August 8, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro

August 8, 2025
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

August 8, 2025
Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.