• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Iyayen Mijina Sun Lakada Masa Duka Lokacin Da Ya Ce Yana Sona – Wata Nakasasshiya

byRabi'u Ali Indabawa
3 years ago
Lakada

Ibeadua Judith Chioma ba ta taba tunanin za ta je makaranta ba a rayuwarta kuma ta auri mutumin da take so, balle ma ta haifi ‘ya’ya. 

Ta yi wannan tunanin ne saboda matar, mai shekara 31, na da nakasa kuma iyayenta sun rasu tun tana ‘yar shekara shida.

  • Da Dumi-Dumi: Jami’an Tsaro Sun Kai Samame Gidan Tukur Mamu
  • Saudiyya Ta Ja Kunnen Netflix Kan Yada Fina-Finan Da Suka Keta Dokokin Musulunci

Judith, wadda ba ta dade da kammala bauta wa kasa a Nijeriya ba (NYSC), ta ce ‘yan mata irinsu suna zuwa makaranta ne kawai idan ba su samu namijin da za su aura ba.

Lokacin da mijinta ya fada wa iyayensa niyyarsa ta auren Judith sai da suka taru suka lakada masa duka har ma suka raunata shi, in ji matashiyar.

‘Ba da lalura aka haife ni ba’ “Ina ‘yar shekara hudu na rasa kafafuwana kuma na gano ba zan iya tafiya ba. Ban san abin da ya faru ba, iyayena za su iya ba da labari amma kuma sun rasu tun ina ‘yar shekara shida,” kamar yadda Judith ta bai wa BBC Pidgin labarinta.

LABARAI MASU NASABA

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Lokacin da iyayenta suka rasu, sai yayarta ta ci gaba da kula da ita kuma ta kai ta makaranta tun daga nazire har zuwa aji uku na karamar sakandare. “‘Yar uwata ce ta dauke ni, ta ci gaba da koya min abubuwa.

Da rarrafe nake zuwa makaranta da coci, na yi ta kuka ina tambayar Allah me ya sa ya yi ni haka cikin irin wannan halin,” in ji ta.

Gwara na mutu da na yi bara a kan titi in ji gurguwa mai sana’ar dinki Lokacin da take JSS1 ne wani malamin Kirista ya saya mata keken guragu.

Bayan ta kai JSS3 kuma sai shugaban makarantar tasu ya ba da shawarar a kai ta makarantar masu bukata ta musamman.

A nan ne rayuwarta ta fara kyautata. Ta hadu da mutanen da rayuwarta ta fi tasu dama-dama, a nan din ne kuma ta hadu da mijin da ta aura.

‘Duk da wuyar da mijina ya sha bai guje ni ba’ Sun hadu da mijinta gaba da gaba a karon farko bayan sun shafe shekara biyu suna magana ta wayar salula.

Damuwar mijin nata da dan uwansa da ya hada su ita ce; ta yaya za ta iya aikin gida da haihuwar yara da kuma karatu bayan iyayensa sun ki amincewa da auren.

Har ma sai da wasu ‘yan uwansa suka doke shi.

Amma a yanzu tana godiya da farin cikin cewa mijin nata bai guje ta ba. “Lokacin da mijina ya ce zai aure ni mahaifiyarsa ta kira mutane don su taimaka mata a zane shi saboda shi kadai ne danta namiji. Suka zane shi sosai har suka raunata shi,” in ji ta.

“Amma duk da wahalar da ya sha bai guje ni ba.”

Ta kara da cewa abin da suka fi damuwa da shi shi ne yadda za ta dauki ciki, idan ma za ta dauka din.

Yanzu haka ta haihu ba cikin sauki ba tare da wata tiyata ba.

Aure, karatu da sauran kalubale Bayan aurensu, mijinta ya shawarce ta ta ci gaba da karatu.

Ta yi aure ne tana ajin ND 2 kuma tana da ciki.

Ta karanci fannin koyarwar kwamfuta wato Computer Education a kwalejin kimiyya, inda ta kammala bayan shekara shida saboda annobar Korona.

“Na samu gurbi a 2015. Na yi karatun shekara shida saboda annobar Korona. Duk da cewa burinta shi ne ta karanta harkar likitanci, “Amma lokacin da muka fara karatun sai suka ce ba sa daukar masu nakasa a sashen likitanci”.

Mun ciro wannan Rahoto daga BBC

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

September 25, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
Al'ajabi

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Next Post
Rayuwar Serena Williams A Fagen Wasan Tennis

Rayuwar Serena Williams A Fagen Wasan Tennis

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version