• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Iyayen Mijina Sun Lakada Masa Duka Lokacin Da Ya Ce Yana Sona – Wata Nakasasshiya

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
in Al'ajabi
0
Iyayen Mijina Sun Lakada Masa Duka Lokacin Da Ya Ce Yana Sona – Wata Nakasasshiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ibeadua Judith Chioma ba ta taba tunanin za ta je makaranta ba a rayuwarta kuma ta auri mutumin da take so, balle ma ta haifi ‘ya’ya. 

Ta yi wannan tunanin ne saboda matar, mai shekara 31, na da nakasa kuma iyayenta sun rasu tun tana ‘yar shekara shida.

  • Da Dumi-Dumi: Jami’an Tsaro Sun Kai Samame Gidan Tukur Mamu
  • Saudiyya Ta Ja Kunnen Netflix Kan Yada Fina-Finan Da Suka Keta Dokokin Musulunci

Judith, wadda ba ta dade da kammala bauta wa kasa a Nijeriya ba (NYSC), ta ce ‘yan mata irinsu suna zuwa makaranta ne kawai idan ba su samu namijin da za su aura ba.

Lokacin da mijinta ya fada wa iyayensa niyyarsa ta auren Judith sai da suka taru suka lakada masa duka har ma suka raunata shi, in ji matashiyar.

‘Ba da lalura aka haife ni ba’ “Ina ‘yar shekara hudu na rasa kafafuwana kuma na gano ba zan iya tafiya ba. Ban san abin da ya faru ba, iyayena za su iya ba da labari amma kuma sun rasu tun ina ‘yar shekara shida,” kamar yadda Judith ta bai wa BBC Pidgin labarinta.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

Lokacin da iyayenta suka rasu, sai yayarta ta ci gaba da kula da ita kuma ta kai ta makaranta tun daga nazire har zuwa aji uku na karamar sakandare. “‘Yar uwata ce ta dauke ni, ta ci gaba da koya min abubuwa.

Da rarrafe nake zuwa makaranta da coci, na yi ta kuka ina tambayar Allah me ya sa ya yi ni haka cikin irin wannan halin,” in ji ta.

Gwara na mutu da na yi bara a kan titi in ji gurguwa mai sana’ar dinki Lokacin da take JSS1 ne wani malamin Kirista ya saya mata keken guragu.

Bayan ta kai JSS3 kuma sai shugaban makarantar tasu ya ba da shawarar a kai ta makarantar masu bukata ta musamman.

A nan ne rayuwarta ta fara kyautata. Ta hadu da mutanen da rayuwarta ta fi tasu dama-dama, a nan din ne kuma ta hadu da mijin da ta aura.

‘Duk da wuyar da mijina ya sha bai guje ni ba’ Sun hadu da mijinta gaba da gaba a karon farko bayan sun shafe shekara biyu suna magana ta wayar salula.

Damuwar mijin nata da dan uwansa da ya hada su ita ce; ta yaya za ta iya aikin gida da haihuwar yara da kuma karatu bayan iyayensa sun ki amincewa da auren.

Har ma sai da wasu ‘yan uwansa suka doke shi.

Amma a yanzu tana godiya da farin cikin cewa mijin nata bai guje ta ba. “Lokacin da mijina ya ce zai aure ni mahaifiyarsa ta kira mutane don su taimaka mata a zane shi saboda shi kadai ne danta namiji. Suka zane shi sosai har suka raunata shi,” in ji ta.

“Amma duk da wahalar da ya sha bai guje ni ba.”

Ta kara da cewa abin da suka fi damuwa da shi shi ne yadda za ta dauki ciki, idan ma za ta dauka din.

Yanzu haka ta haihu ba cikin sauki ba tare da wata tiyata ba.

Aure, karatu da sauran kalubale Bayan aurensu, mijinta ya shawarce ta ta ci gaba da karatu.

Ta yi aure ne tana ajin ND 2 kuma tana da ciki.

Ta karanci fannin koyarwar kwamfuta wato Computer Education a kwalejin kimiyya, inda ta kammala bayan shekara shida saboda annobar Korona.

“Na samu gurbi a 2015. Na yi karatun shekara shida saboda annobar Korona. Duk da cewa burinta shi ne ta karanta harkar likitanci, “Amma lokacin da muka fara karatun sai suka ce ba sa daukar masu nakasa a sashen likitanci”.

Mun ciro wannan Rahoto daga BBC


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AureDukaIyayen MijiNakasasshiyaSabawa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasuwannin Jihar Legas Sun Bunkasa A Karkashin Jagorancinmu –Shehu Samfam

Next Post

Rayuwar Serena Williams A Fagen Wasan Tennis

Related

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi
Al'ajabi

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

1 week ago
An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano
Al'ajabi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

1 month ago
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa

1 month ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi

2 months ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Mahaifiyarsa Da Taɓarya A Bauchi

3 months ago
‘Yansanda Sun Dakile Harin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Kan Wasu Rukunin Gidaje A Katsina
Al'ajabi

Wani Jami’in Ɗansanda Ya Bindige Kansa Har Lahira A Jihar Nasarawa

4 months ago
Next Post
Rayuwar Serena Williams A Fagen Wasan Tennis

Rayuwar Serena Williams A Fagen Wasan Tennis

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.