ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Iyayen Mijina Sun Lakada Masa Duka Lokacin Da Ya Ce Yana Sona – Wata Nakasasshiya

by Rabi'u Ali Indabawa
4 years ago
Lakada

Ibeadua Judith Chioma ba ta taba tunanin za ta je makaranta ba a rayuwarta kuma ta auri mutumin da take so, balle ma ta haifi ‘ya’ya. 

Ta yi wannan tunanin ne saboda matar, mai shekara 31, na da nakasa kuma iyayenta sun rasu tun tana ‘yar shekara shida.

  • Da Dumi-Dumi: Jami’an Tsaro Sun Kai Samame Gidan Tukur Mamu
  • Saudiyya Ta Ja Kunnen Netflix Kan Yada Fina-Finan Da Suka Keta Dokokin Musulunci

Judith, wadda ba ta dade da kammala bauta wa kasa a Nijeriya ba (NYSC), ta ce ‘yan mata irinsu suna zuwa makaranta ne kawai idan ba su samu namijin da za su aura ba.

ADVERTISEMENT

Lokacin da mijinta ya fada wa iyayensa niyyarsa ta auren Judith sai da suka taru suka lakada masa duka har ma suka raunata shi, in ji matashiyar.

‘Ba da lalura aka haife ni ba’ “Ina ‘yar shekara hudu na rasa kafafuwana kuma na gano ba zan iya tafiya ba. Ban san abin da ya faru ba, iyayena za su iya ba da labari amma kuma sun rasu tun ina ‘yar shekara shida,” kamar yadda Judith ta bai wa BBC Pidgin labarinta.

LABARAI MASU NASABA

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar

Lokacin da iyayenta suka rasu, sai yayarta ta ci gaba da kula da ita kuma ta kai ta makaranta tun daga nazire har zuwa aji uku na karamar sakandare. “‘Yar uwata ce ta dauke ni, ta ci gaba da koya min abubuwa.

Da rarrafe nake zuwa makaranta da coci, na yi ta kuka ina tambayar Allah me ya sa ya yi ni haka cikin irin wannan halin,” in ji ta.

Gwara na mutu da na yi bara a kan titi in ji gurguwa mai sana’ar dinki Lokacin da take JSS1 ne wani malamin Kirista ya saya mata keken guragu.

Bayan ta kai JSS3 kuma sai shugaban makarantar tasu ya ba da shawarar a kai ta makarantar masu bukata ta musamman.

A nan ne rayuwarta ta fara kyautata. Ta hadu da mutanen da rayuwarta ta fi tasu dama-dama, a nan din ne kuma ta hadu da mijin da ta aura.

‘Duk da wuyar da mijina ya sha bai guje ni ba’ Sun hadu da mijinta gaba da gaba a karon farko bayan sun shafe shekara biyu suna magana ta wayar salula.

Damuwar mijin nata da dan uwansa da ya hada su ita ce; ta yaya za ta iya aikin gida da haihuwar yara da kuma karatu bayan iyayensa sun ki amincewa da auren.

Har ma sai da wasu ‘yan uwansa suka doke shi.

Amma a yanzu tana godiya da farin cikin cewa mijin nata bai guje ta ba. “Lokacin da mijina ya ce zai aure ni mahaifiyarsa ta kira mutane don su taimaka mata a zane shi saboda shi kadai ne danta namiji. Suka zane shi sosai har suka raunata shi,” in ji ta.

“Amma duk da wahalar da ya sha bai guje ni ba.”

Ta kara da cewa abin da suka fi damuwa da shi shi ne yadda za ta dauki ciki, idan ma za ta dauka din.

Yanzu haka ta haihu ba cikin sauki ba tare da wata tiyata ba.

Aure, karatu da sauran kalubale Bayan aurensu, mijinta ya shawarce ta ta ci gaba da karatu.

Ta yi aure ne tana ajin ND 2 kuma tana da ciki.

Ta karanci fannin koyarwar kwamfuta wato Computer Education a kwalejin kimiyya, inda ta kammala bayan shekara shida saboda annobar Korona.

“Na samu gurbi a 2015. Na yi karatun shekara shida saboda annobar Korona. Duk da cewa burinta shi ne ta karanta harkar likitanci, “Amma lokacin da muka fara karatun sai suka ce ba sa daukar masu nakasa a sashen likitanci”.

Mun ciro wannan Rahoto daga BBC

Lakada
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas
Al'ajabi

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

April 21, 2026
Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar
Al'ajabi

Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar

March 8, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Al'ajabi

Ɓata-gari Sun Kashe Matar Aure Da ’Ya’yanta 3 A Kano

January 21, 2026
Next Post
Rayuwar Serena Williams A Fagen Wasan Tennis

Rayuwar Serena Williams A Fagen Wasan Tennis

LABARAI MASU NASABA

An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

June 5, 2026
Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

June 5, 2026
Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 5, 2026
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

June 5, 2026
Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.