ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saudiyya Ta Ja Kunnen Netflix Kan Yada Fina-Finan Da Suka Keta Dokokin Musulunci

by Sadiq
4 years ago
Saudiyya

Kasashen Larabawa na yankin Gulf sun nemi kamfanin Netflix ya cire dukkan fina-finan da suka sabawa dokokin Musulunci da al’adun tarbiyya, kamar yadda kafar yada labarai ta Saudiyya ta ruwaito.

A wata sanarwa da kungiyar kasashen yankin Gulf ta fitar ta yi gargadi cewar wasu fina-finai na baya-bayan nan da aka yi don yara sun saba wa dokokin musulunci.

  • Lauyoyi Sun Maka Ado Gwanja, Safara’u, 442 Da Wasu ‘Yan TikTok A Kotu
  • Buhari Ya Kaddamar Da Wani Kwamiti Da Zai Sake Duba Bukatun Kungiyar ASUU

Kafar talabijin ta Saudiyya ta nuna wasu bidiyo da aka dusaseh fuskarsu na katun din fim din Jurassic World: Camp Cretaceous, wanda aka nuna wasu yara mata biyu suka nuna suna son juna tare da sumbatar juna.

ADVERTISEMENT

Gidan talabijin na Al Ekhbariya da ya nuna wani sashe na fim din da wani kamfanin Faransa na Cuties ya shirya, ya sanya take kamar haka “bidiyon da ke nuna rashin da’a da rusa tarbiyya wanda ke barazanar lalata tarbiyyar yara.”

A wani bidiyon da Al Ekhbariya ta wallafa a shafinta na Intanet, ta yi zargin cewa fim din na “yada luwadi da madigo ne.”

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Hakazalika gidan talabijin din ya yi hira da mutane da dama da suka yi irin wanan zargin tare da kiran hukumomi su dauki mataki cikin gaggawa.

An tuntubi Netflix da ya cire bidiyon, da kuma duk wasu fina-finai da aka shirya don yara, tare da tabbatar da bin dokoki,” kamar yadda sanarwar hadin gwiwa daga hukumar kula da fina-finai ta Saudiyya da ta kula da kafafen yada labarai.

Hukumomi za su sa ido don ganin ko an bi umarnin, tare da daukar matakan shari’a idan har aka ci gaba da yada fina-finan”, kamar yadda suka yi gargadin.

Babu wani martani daga kamfanin Netflix, duk da cewa Saudiyya ba ta da wasu dokoki na damar zabar jinsi, amma yin luwadi da madigo da zina haramun ne a kasar.

A karkashin dokokin Musulunci na kasar dai, hukuncin duk wanda aka kama da laifin luwadi ko madigo hukuncin kisa ne ko bulala, ya dangata girman laifin.

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Ana Zargin Budurwa Da Kashe Mahaifiyar Saurayinta Da Adda A Kamaru

Ana Zargin Budurwa Da Kashe Mahaifiyar Saurayinta Da Adda A Kamaru

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.