• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jagororin Siyasar Arewa Raunana Ne Kuma A Rarrabe Suke – Salihu Lukman

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
1 year ago
arewa

Tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar APC a yankin arewa maso yamma, Salihu Lukman ya ce shugabannin siyasar arewa raunana ne kuma kawunansu rabe suke ba su da tsari.

A wata budaddiyar wasika da ya aike wa shugabannin a ranar Lahadi, Lukman ya ce ko shi kansa mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ba ya kare muradin arewacin Nijeriya.

  • Muna Jaddada Kiran A Tsame Masarautunmu Daga Rikicin Siyasa
  • Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Hutun Sabuwar Shekarar Musulunci

A cewarsa, yawancin shugabannin arewa sun damu da kare muradinsu ne kawai a cikin gwamnati.
“Babu shakka, shugabannin siyasar arewa suna kara rauni da rashin tsari. Hatta shi kansa mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, wanda shi ne babban mai rike da mukami a yankin arewa, ya kamata ya zama shugaban siysa a arewa.

“Tare da mutuntawa, zai yi wahala duk wani jami’in gwamnatin Asiwaju Tinubu daga arewa ciki har da Shettima ya yi kasada wajen kare muradun arewa.

“Abin takaici, yawancin shugabannin arewa sun fi damuwa da kare muradin kansu a cikin gwamnati.
“Saboda kariyar kai, tuni aka fara makircin zaben 2027. A cikin fadar shugaban kasa akwai alamun yakin, wanda ake zargin zai taso ne daga bangaren shugaban kasa.”

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

Lukman ya kara da cewa shugabannin arewa a jam’iyyun adawa su ma ba su dace ba, saboda sun fi mayar da hankali ne kawai wajen tsayawa takara a zaben 2027.

“Ya kamata mu ja kunnen shugabannin siyasa a kasar nan, saboda abubuwa na gab da kwace musu musamman a arewa.

“Idan ba a kula ba, yunwa da ta karade ko’ina a arewa zai iya sa mutane su fara shiga gidajen al’umma da wawashe dukiyoyinsu.

Lukman ya ce dole ne ‘yan Nijeriya su hada kai wajen samar da sabbin tsarin siyasa masu tasiri domin amfanin kasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
An Nada Ibrahim Rilwan A Matsayin Sabon Garkuwan Matasan Arewa

An Nada Ibrahim Rilwan A Matsayin Sabon Garkuwan Matasan Arewa

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.