ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Nada Ibrahim Rilwan A Matsayin Sabon Garkuwan Matasan Arewa

by Sulaiman and Shehu Yahaya
2 years ago
Arewa

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Kungiyar Dalibban Nijeriya da hadin gwiwar kungiyar Matasan Arewa sun karrama Malam Ibrahim Rilwan Mohammed (Shugaban Gidauniyar IRM) a Matsayin Garkuwan Matasan Arewa.

Taron Wanda ya gudana a dakin taro na gidan Tarihi ( Arewa House) da ke Kaduna, kungiyar ta bukaci masu Hannu da shuni da su rika taimakawa marasa galihu a cikin al’umma.

  • Harin Gwoza: Gwamnonin Arewa Sun Bukaci Dakile ‘Yan Ta’adda Duk Inda Suke
  • Lamunin Naira Biliyan 5 Ga ‘Yan Fim: Yaushe Kannywood Za Ta Samu Nata?

A jawabinsa Mataimakin Shugaban Majalisar dalibban Nijeriya ( NANS) Kwamared Kabiru Aminu ya bayyana cewa an zabi wanda za a karramawar ne saboda dimbin gudumuwarsa ga ci gaban dalibban da kuma matasan Nijeriya a kowanne mataki. Bugu da kari ya bayyana namijin kokarin wanda aka karrama wajen sha’anin kyautata rayuwar mata da matasa ta hanyar sana’o’in hannu domin su kasance masu dogaro ga kawunan su a cikin garuruwan su, yana mai cewa irin kyakkyawar rawar da gidauniyar sa take takawa wajen daukaka Kalmar Allah ta hanyar ginin Masallatan Jumma’a da na Hamsar Sallawati da kuma Makarantun Islamiyya a birane da karkara a kowanne yankin dake cikin kasarnan da kuma Nijar.
Ya bayyana Malam Ibrahim Rilwan Mohammed a matsayin mai tsoron Allah da gudun duniya kari ga karimcinsa musamman ga marasa galihu.

ADVERTISEMENT

A nasa jawabin Shugaban kungiyar Matasan Arewa (Arewa Youth Forum for Liberty) Abdulmalik Zakari ya bayyana cewa kungiyar tayi bincike mai zurfi wajen tantace mutane masu kokari da dawainiyar mutane ba tare da gajiyawa ba.
Ya kara da cewa samun irinsa ya yi wuya a yankin Arewa balle kuma a kasar bakidaya. Ya bayyana cewa Lambar Yabon da Sarautar Garkuwan Matasan Arewa za su karfafa masa gwiwa domin ya ci gaba da aiwatar da ayyukan alheri domin wasu su yi koyi dashi.
A cikin jawabinsa wani malamin Addinin Musulunci Farfesa Mansur Yalwa ya shawarci sabon Garkuwan Matasan Arewa da ya ci gaba da gudanar da ayyukan alheri domin Allah ba domin fadanci ba. Ya yabawa wadanda suka shirya taron saboda karrama mutane irin su Malam Ibrahim Rilwan Mohammed da su ke bayar da babbar gudumuwa wajen daukaka Kalmar Allah musamman abinda ya shafi sha’anin Ilimin Addinin Musulunci da Ilimin Zamani a kowanne mataki.
Da yake jawabi Shugaban Gidauniyar IRM kuma sabon Garkuwan Matasan Arewa Malam Ibrahim Rilwan Mohammed ya bayyana godiyarsa ga Kungiyar dalibban Nijeriya da kungiyar Matasan Arewa da suka zabe shi domin bashi Lambar Yabo da Sarautar Garkuwan Matasan Arewa. Ya bayyana cewa a matsayin sa na Musulmi ya yi daidai ya taimakawa mutane saboda yana daya daga cikin koyarwar Musulunci, ya bayyana cewa saboda haka yake taimako saboda Allah.
Ya bayyana cewa a shigo wani lokaci da mutane ba su taimakon makota KO ‘yan uwan su, kuma idan an ga wani na taimakon al’umma sai a danganta haka da cewa yana son wani mukamin siyasa ne. “Ina tabbata maku cewa ba domin siyasa ko son wani mukamin siyasa nake yin wannan taimako ba”.

Arewa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • Sulaiman
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Arewa
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Bayan Shehu Sani Ya Ƙalubalanci Zailani, Rikicin APC Ya Ƙara Zafi A Kaduna

MASU ALAKA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
Labarai

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
Labarai

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Next Post
An Fara Kashe Kudi A Firimiyar Ingila

An Fara Kashe Kudi A Firimiyar Ingila

LABARAI MASU NASABA

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.